ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Zamfara Ta Lashe Gasar AlKur’ani Ta Ƙasa Ta Mata

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Gasar

Maryam Abdullahi daga Jihar Zamfara ta lashe gasar karatun Al-Qur’ani ta ƙasa karo na 14 ta Mata na makarantun sakandare marasa koyar da harshen Larabci a Nijeriya.

Gasar wacce ƙungiyar RIBADA te shiryawa tare da haɗin gwuiwar gwamnatin Jihar Katsina, inda ‘yan takara daga jihohi daban-daban suka fafata wajen haddace Hizifi 60, da 40, da 20, da 10, da kuma hizifi biyu.

  • Ba Mu Da Hannu A Kisan Isma’il Haniyeh – Amurka
  • Kasurgumin Dan Ta’adda Ya Mika Wuya Ga Sojoji A Borno

Maƙasudin Gasar

ADVERTISEMENT

Sheikh Shu’aibu Shehu, Shugaban ƙungiyar na ƙasa, ya bayyana cewa gasar na da nufin ƙarfafa haddar Al-Qur’ani da kuma nazarin sa tsakanin ‘yan mata a makarantun sakandare marasa koyar da harshen Larabci.

Ya kara da cewa gasar farko ta gudana ne a Kano a shekarar 2012, yayin da Katsina te zama jiha ta 14 da ta karɓi baƙuncin gasar.

LABARAI MASU NASABA

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Sheikh Shehu ya yi kira ga ɗalibai da su ci gaba da neman ilimi tare da bin koyarwar Al-Qur’ani.

Kwamishinan Ilimi na Jihar Katsina, Hajiya Zainab Musawa, da Mataimakin Gwamnan Jihar, Malam Faruk Lawal-Jobe, sun yaba wa masu shirya gasar tare da tabbatar da goyon bayan su ga ilimin ‘yan mata.

Sauran waɗanda suka yi nasara daga rukunoni daban-daban na gasar su ne: Farida Zakariyya daga Jihar Kaduna ta lashe hizifi 40, da Aisha Sa’ad daga Katsina ta lashe hizifi 20, da Maimuna Adam-Jibril daga Borno ta lashe hizifi 10, yayin da Fatima Adam daga Jigawa ta lashe hizifi biyu.

Kyaututtukan da ka rabar sun haɗa da firiji, da Keken ɗinki, da barguna, da kayan sawa, da kuɗi.

Dr. Aliyu Abdullahi, Shugaban ƙungiyar na ƙasa, ya yi alkawarin ɗaukar nauyin wacce ta zo ta ɗaya zuwa Umrah.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Labarai

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Next Post
An Tarwatsa Masu Zanga-zanga Kan Kokarin Kunna Wuta A Kofar Gidan Gwamnatin Kano

An Tarwatsa Masu Zanga-zanga Kan Kokarin Kunna Wuta A Kofar Gidan Gwamnatin Kano

LABARAI MASU NASABA

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.