• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohi Sun Kashe Naira Biliyan 139.92 Wajen Biyan Bashin Kasashen Ketare A Wata 6

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
1 year ago
Bashi

Jihohin Nijeriya sun kashe naira biliyan 139.92 daga cikin kudaden da suka karba a wurin gwamnatin tarayya a watanni 6 na farkon shekarar 2024.

 

Wannan bayanai dai yana kunshe a cikin kididdigan da kwamitin asusun rarraba kudade ta tarayya wacce ta samu daga bayanan hukumuar kididdiga ta kasa (NBS).
Kudaden da aka kashe ya kkaru da kashi 122% daga naira biliyan 63.06 da aka kashe a shekarar da ta gabata na watanni shidar farkon shekara.

  • Yadda Mutane Ke Tona Ramin Tururuwa Don Neman Abinci A Borno
  • An Yi Watsi Da Ayyuka Na Fiye Da Naira Tiriliyan 17 A Nijeriya – Cibiyar CIPMN

Bayanan ya nuna cewa jihohin sun kashe naira biliyan 9 zuwa naira biliyan 20 a kowacce wata, wanda ya ninka bashin da ake bi sakamakon faduwar darajar naira.
A watan Janairun 2024, jihohin Nijeriya sun kashe naira biliyan 9.88 wajen biyan basussuka a waje, wanda ya ragu daga naira biliyan 13.7 a watan Janairun 2023. A nan an sami ragowar kashi 27.7%, wanda yake nuna cewa wasu jihohi ba su da basussukan sosai.

 

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Haka kuma canjin dala na tsakanin naira 830 zuwa 1,000 wanda shi ne mafi kankanta a wannan rahoton.

A watan Fabrarun 2024 kuwa, an biya bashin naira biliyan 24.53, wanda aka sami karin kashi 148%, inda ya karu daga naira biliyan 9.88 na watan Fabrarun 2023.

 

A watan Maris 2024, an biya bashin naira biliyan 40.41, wanda hakan ke alamta cewa an sami karin kashe 309%, idan aka kwatanta da watan Maris ta 2023 da aka biya naira bilyan 9.88.

 

Daga watan Afrilu zuwa Yuni shekara ta 2024, jimillar bashin da aka biya shi ne, naira biliyan 21.70 a kowacce wata idan aka kwatanta da naira biliyan 9.88 da aka biya na shekarar 2023, kudin da aka kashe ya karu da kashi 119.70% a kowacce wata.

 

Jihohin Kaduna da Lagos su ne suka fio biyan bashi a kan kowacce jiha, don bashin da jihohin suka biya ya karu daga naira biliyan 16.88 a watannin shida na farkon shekarar 2023, inda a yanzu ya koma naira biliyan 32.44 a wannan shekarar ta 2024, Kenan an sami karin kashi 92%, wadannan jihohin guda biyu sun kashi 40% na bashin da ake binsu.

 

Haka kuma jihohin Kuros Ribas da Bauchi sun sami karin bashin da ake binsu. Inda Kuros Ribas ta biya Naira biliyan 2.21 a shekarar 2023 a wannan shekarar kuwa ya koma naira biliyan 7.87, an sami karin kashi 256%. A yayin da Jihar Bauchi a shekarar 2023 sun biya naira biliyan 3.28 a wannan shekarar kuwa sun biya naira biliyan 6.33 hakan na nuna cewa an sami karin kashi 93%.

 

Jihar Ogun sun sami karin biyan bashi a kasashen waje daga naira biliyan 1.57 a shekarar 2023 zuwa naira biliyan 4.29 a shekarar 2024, wanda aka sami karin kashi 173%, haka lamarin yake a Jihar Oyo inda abun ya karu daga naira biliyan 2.61 a shekarar 2023, ya koma naira biliyan 6.36 a shekarar 2024 wanda ke nuna an sami karin kashi 144%.

 

Jihar Ribas ma haka take don an sami karuwar bashi a kasashen waje daga naira biliyan 1.76 da aka biya a watannin shidar farkon shekara ta 2023 zuwa naira biliyan 4.62 a watanni shidar farkon shekara ta 2024, wanda ke nuna cewa an sami karin kashi 162% idan aka kwatanta shekarun.

 

Wadannan bayanan sun kara nuna yadda kudaden da Nijeriya ke samu suke karewa wajen biyan basussuka a waje.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
Manyan Labarai

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro
Manyan Labarai

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Next Post
Na Yi Mamakin Ganin Takardar Tuɓe Rawanina Na Sarautar Mujaddadin Bauchi – Sanata Buba

Na Yi Mamakin Ganin Takardar Tuɓe Rawanina Na Sarautar Mujaddadin Bauchi - Sanata Buba

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

November 3, 2025
Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

November 3, 2025
Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

November 3, 2025
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.