ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Majalisa

Kwamitin Majalisar Dattawa kan gyaran kundin tsarin mulki na 1999, ya shirin gudanar da taron sauraron jin ra’ayoyin jama’a a wasu sassan Nijeriya na kwanaki biyu, domin tattara bayanai kan kiraye-kirayen kudirin gyara kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Kwamitin, wanda ke karkashin jagorancin mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya bayyana a cikin wani sanarwa da aka fitar a Abuja, cewa sauraron jin ra’ayoyin al’umma zai gudana Legas (Kudu maso yamma), Inugu (Kudu maso gabas), Ikot Ekpene (Kudu maso yamma), Jos (Arewaci ta tsakiya), Maiduguri (Arewaci ta Gabas) da Kano (Arewaci ta yamma).

  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • Firaministan Singapore: Jama’ar Sin Suna Da Kwarewar Kirkire-Kirkiren Fasahohi

Kamar yadda aka bayyana a cikin sanarwar da ke dauke da sa hannun mai ba da shawara na musamman kan kafofin watsa labarai na mataimakin shugaban majalisar datta, Ismail Mudashir, sauraron jin ra’ayoyin zai gudana ne a ranakun 4 da 5 ga Yuli, 2025 a wurare daban-daban da aka tanada.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kara da cewa sauraron jin ra’ayoyin jama’a, zai binciki muhimman batutuwa na kasa nan, ciki har da ‘yancin bai wa kananan hukumomi da gyare-gyaren zabe da na bangaren shari’a da kirkirar jihohi da ‘yansandan jihohi da kuma manufofin gwamnati.

Daya daga cikin kudirorin da aka fayyace a cikin sanarwar, yana ba da shawarar kafa majalisin kananan hukumomi a matsayin mataki na uku na gwamnatin tarayya don tabbatar da kasancewarsu cikin dimokuradiyya da kuma tsawon wa’adin mulkinsu.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

Bisa ga sanarwar, wannan wani sashe ne na sabon yunkuri na ba da cikakken ‘yanci ga majalisar kananan hukumomi 774 na kasar nan.

Haka kuma a kan gyaran kananan hukumomi, wata kudirin doka da ke neman kirkiro wata hukumar zabe mai zaman kanta ta kananan hukumomi (NALGEC), wanda za ta dunga shiryawa, gudanar da kuma kula da zaben kananan hukumomin, za a kuma gabatar da ita ga ‘yan Nijeriya don yin nazari a taron sauraron jin ra’ayoyin.

Wadansu batutuwa da aka fitar a cikin sanarwar da suka hada da kudirin dokoki guda biyu kan tsaro da manufar samar da ‘yansandan jihohi da majalisar tsaro na jihohi don tsara manufofin tsaro na cikin gida a matakin yankuna.

“A bangaren gyaran manufifin kudade kuwa, za a duba dokoki guda shida ciki har da dokar da za ta ba da iko ga hukumar rarraba haraji ta kasa don tilasta bin doka da rarraba kudaden haraji daga asusun gwamnatin tarayya da kuma inganta tsarin nazarin hanyar rarraba kudaden.

“A cikin wata sabuwar mataki tare da magance rashin daidaiton jinsi, kwamitin zai kuma yi nazarin wata doka da za ta samar da karin kujeru ga mata a cikin majalisun tarayya da majalisun jihohi.

“Don karfafa masarautun gargajiya, za a duba wani kudirin doka za sauya kundin tsarin mulki domin kafa majalisar masarautu gargajiya ta kasa da majalisar masarautun gargajiya ta jihohi da majalisar masarautun gargajiya ta kananan hukumomi.

“A kan gyaran tsarin zabe kuwa, za a tattauna wani shawarwari da ke neman gyara kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 don ba da damar tsayawa takara kai tsaye a kowane mataki na zabe, daga kananan hukumomi zuwa shugabancin kasa a taron sauraron jin ra’ayoyin.

“Jimlar wasu kudirorin doka fiye da 20 da ke neman gyara tsarin shari’a na kasar, ciki har da lokacin da ake zartar da hukunci da kuma fadada ikon kotunan zabe, suna daga cikin batutun da za a duba.

“Shawarwari guda talatin da daya kan kirkiro jihohi, suna cikin batutun da za a dubawa a taron sauraron jin ra’ayoyin.”

Kwamitin ya jaddada muhimmancin shigar jama’a wajen tsara kundin tsarin mulkin kasar, ya yi kira ga kowa da ya halarci taron sauraron jin ra’ayin jama’a na yankin.

Majalisa
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna
Siyasa

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Next Post
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki - Sanata Kaita 

LABARAI MASU NASABA

Majalisa

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.