ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Majalisa

Kwamitin Majalisar Dattawa kan gyaran kundin tsarin mulki na 1999, ya shirin gudanar da taron sauraron jin ra’ayoyin jama’a a wasu sassan Nijeriya na kwanaki biyu, domin tattara bayanai kan kiraye-kirayen kudirin gyara kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Kwamitin, wanda ke karkashin jagorancin mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya bayyana a cikin wani sanarwa da aka fitar a Abuja, cewa sauraron jin ra’ayoyin al’umma zai gudana Legas (Kudu maso yamma), Inugu (Kudu maso gabas), Ikot Ekpene (Kudu maso yamma), Jos (Arewaci ta tsakiya), Maiduguri (Arewaci ta Gabas) da Kano (Arewaci ta yamma).

  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • Firaministan Singapore: Jama’ar Sin Suna Da Kwarewar Kirkire-Kirkiren Fasahohi

Kamar yadda aka bayyana a cikin sanarwar da ke dauke da sa hannun mai ba da shawara na musamman kan kafofin watsa labarai na mataimakin shugaban majalisar datta, Ismail Mudashir, sauraron jin ra’ayoyin zai gudana ne a ranakun 4 da 5 ga Yuli, 2025 a wurare daban-daban da aka tanada.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kara da cewa sauraron jin ra’ayoyin jama’a, zai binciki muhimman batutuwa na kasa nan, ciki har da ‘yancin bai wa kananan hukumomi da gyare-gyaren zabe da na bangaren shari’a da kirkirar jihohi da ‘yansandan jihohi da kuma manufofin gwamnati.

Daya daga cikin kudirorin da aka fayyace a cikin sanarwar, yana ba da shawarar kafa majalisin kananan hukumomi a matsayin mataki na uku na gwamnatin tarayya don tabbatar da kasancewarsu cikin dimokuradiyya da kuma tsawon wa’adin mulkinsu.

LABARAI MASU NASABA

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

Bisa ga sanarwar, wannan wani sashe ne na sabon yunkuri na ba da cikakken ‘yanci ga majalisar kananan hukumomi 774 na kasar nan.

Haka kuma a kan gyaran kananan hukumomi, wata kudirin doka da ke neman kirkiro wata hukumar zabe mai zaman kanta ta kananan hukumomi (NALGEC), wanda za ta dunga shiryawa, gudanar da kuma kula da zaben kananan hukumomin, za a kuma gabatar da ita ga ‘yan Nijeriya don yin nazari a taron sauraron jin ra’ayoyin.

Wadansu batutuwa da aka fitar a cikin sanarwar da suka hada da kudirin dokoki guda biyu kan tsaro da manufar samar da ‘yansandan jihohi da majalisar tsaro na jihohi don tsara manufofin tsaro na cikin gida a matakin yankuna.

“A bangaren gyaran manufifin kudade kuwa, za a duba dokoki guda shida ciki har da dokar da za ta ba da iko ga hukumar rarraba haraji ta kasa don tilasta bin doka da rarraba kudaden haraji daga asusun gwamnatin tarayya da kuma inganta tsarin nazarin hanyar rarraba kudaden.

“A cikin wata sabuwar mataki tare da magance rashin daidaiton jinsi, kwamitin zai kuma yi nazarin wata doka da za ta samar da karin kujeru ga mata a cikin majalisun tarayya da majalisun jihohi.

“Don karfafa masarautun gargajiya, za a duba wani kudirin doka za sauya kundin tsarin mulki domin kafa majalisar masarautu gargajiya ta kasa da majalisar masarautun gargajiya ta jihohi da majalisar masarautun gargajiya ta kananan hukumomi.

“A kan gyaran tsarin zabe kuwa, za a tattauna wani shawarwari da ke neman gyara kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 don ba da damar tsayawa takara kai tsaye a kowane mataki na zabe, daga kananan hukumomi zuwa shugabancin kasa a taron sauraron jin ra’ayoyin.

“Jimlar wasu kudirorin doka fiye da 20 da ke neman gyara tsarin shari’a na kasar, ciki har da lokacin da ake zartar da hukunci da kuma fadada ikon kotunan zabe, suna daga cikin batutun da za a duba.

“Shawarwari guda talatin da daya kan kirkiro jihohi, suna cikin batutun da za a dubawa a taron sauraron jin ra’ayoyin.”

Kwamitin ya jaddada muhimmancin shigar jama’a wajen tsara kundin tsarin mulkin kasar, ya yi kira ga kowa da ya halarci taron sauraron jin ra’ayin jama’a na yankin.

Majalisa
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

MASU ALAKA

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Atiku
Siyasa

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

July 2, 2026
‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi
Manyan Labarai

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

July 1, 2026
Next Post
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki - Sanata Kaita 

LABARAI MASU NASABA

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar

July 5, 2026
Dalilan Da Suka Jawo Aka Ƙi Yin Maraba Da FIM House A Jihar Kano

Dalilan Da Suka Jawo Aka Ƙi Yin Maraba Da FIM House A Jihar Kano

July 5, 2026
Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

July 5, 2026
Zulum Ya Bayar Da Cak Na Naira Biliyan 5.81 Domin Biyan Bashin Garatutin Ma’aikata Masu Ritaya

Zulum Ya Bayar Da Cak Na Naira Biliyan 5.81 Domin Biyan Bashin Garatutin Ma’aikata Masu Ritaya

July 5, 2026
Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 5, 2026
Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

July 5, 2026
Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

July 5, 2026
Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.