ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafafen Yaɗa Labarai Ne Manyan Dirkokin Dimokraɗiyyarmu – Minista

by yahuzajere
2 years ago
labarai

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya sake jaddada ƙudirin wannan gwamnati wajen bai wa kafafen yaɗa labarai ‘yancin su, ba tare da takunkumi ko dabaibayi ba.

Ya ce kafafen yaɗa labarai sun taka muhimmiyar wajen tabbatar da kafuwar turakun dimokiraɗiyyar ƙasar nan, don haka abu ne da ya zama dole a a yi riƙo da kafafen yaɗa labarai saboda tasirin su.

Ministan ya bayyana haka ne a ranar Talata, lokacin da ya karɓi baƙuncin shugabannin Cibiyar Kare Haƙƙin Jaridu da ‘Yan Jarida ta Duniya (IPI), a ƙarƙashin shugaban ta, kuma Babban Editan jaridar Premium Times, Alhaji Musikilu Mojeed.

ADVERTISEMENT

IPI ta kai ziyara ne a ranar Talata, 19 ta Disamba, a ofishin ministan da ke Abuja.

IPI ƙungiya ce ta manyan editocin jaridu na duniya, masu kafafen yaɗa labarai da kuma fitattun ‘yan jarida.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Funkason Fulawa

Yadda Ake Yin Pizza A Gida

Babban dalilin kafa ƙungiyar shi ne kare haƙƙin aikin jarida tare da tsayawa kan kare aikin jarida da ‘yan jarida daga dukkan wata barazanar da ka iya tunkarar su.

Ministan ya ƙara nanata matsayar Shugaba Tinubu dangane da ‘yancin kafafen yaɗa labarai, tare da cewa shi kan sa shugaban tsohon ɗan gwagwarmayar kare ‘yancin dimokiraɗiyya ne, don haka ya na da dukkan ruwa da tsaki wajen nuna goyon bayan ‘yancin kafafen yaɗa labarai da ‘yan jarida.

Kuma ya yi alƙawari cewa gwamnatin sa ba za ta taɓa yi wa aikin jarida ƙarfa-ƙarfa ba.

Idris ya ce dimokiraɗiyya a Nijeriya na buƙatar nagartacciyar alƙibla, wadda kuma gwamnati ke neman gudunmawar dukkan masu karsashin ƙara mata nagarta, ciki kuwa har da jaridu, kafafen yaɗa labarai da ‘yan jarida su kan su.

Ya ce yi wa wannan tsari garambawul nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa da kowa, a dunƙule.

Daga nan ya yi yabo da jinjina ga shugaban IPI dangane da zaɓen sa da aka yi ya jagoranci cibiyar.

Ya yi kira ga Mojeed da ya yi amfani da ƙwarewar sa ta aikin jarida wajen yi wa IPI kyakkyawan jagoranci.

Tun da farko, sai da Shugaban na IPI, Musikilu Mojeed, ya shaida wa ministan cewa a yanzu ana samun cigaba a farfajiyar kafafen yaɗa labarai, don haka ana yi wa aikin jarida kyakkyawar fata nagari.

Daga nan ya yi kira ga gwamnati da ta tabbatar da kare rayuka da lafiyar ‘yan jarida a duk inda suke aiki.

 

  • Abin Da Ya Sa Nijeriya Ke Durkushewa

Ya kuma tabbatar wa da Idris cewa IPI za ta ba shi goyon baya, musamman kasancewa ya na ɗaya daga cikin membobin farko da su ka kafa cibiyar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ake Funkason Fulawa
Girke-Girke

Yadda Ake Funkason Fulawa

December 20, 2025
Yadda Ake Yin Pizza A Gida
Girke-Girke

Yadda Ake Yin Pizza A Gida

December 14, 2025
Yadda Ake Yin Pizza A Gida
Girke-Girke

Yadda Ake Yin Pizza A Gida

December 7, 2025
Next Post
Kiran Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labarun Nijeriya Ga Duniya 

Kiran Minista Ga VON: Ku Yaɗa Kyawawan Labarun Nijeriya Ga Duniya 

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.