• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Da Zaben Gwamnonin Imo, Kogi Da Bayelsa Ke Fuskanta

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Kalubalen Da Zaben Gwamnonin Imo, Kogi Da Bayelsa Ke Fuskanta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanaki kadan ya rage a gudanar da zaben gwamna a jihohin Kogi, Imo da Bayelsa, sai dai akwai wasu kalubale da zabukan ka iya fuskanta, musamman na rashin tsaro da kaurace wa zaben da kuma yadda hukumar zabe mai zaman kanta za ta iya gudanar da sahihin zabe a daukacin jihohin ba tare da wata matsala ba.

Shi ya sa ma, tsohon shugaban kasa, Abdulsalami Abubakar da, Rabaran Mathew Hassan Kukah, sun yi kira ga daukacin ‘yan takara da magoya baya da su yi kokarin wajen gudanar da zabukan ba tare da tashe-tashen hankula ba.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da manyan ‘yan takarar gwamna a jihohin suke cacar baki tare da sukar juna, wanda hakan na iya haddasa tashe-tashen hankula a jihohinsu.

A yayin da zaben gwamna a jihohin uku zai gudana a ranar 11 ga watan Nuwamba, 2023, kwamitin zaman lafiya na kasa karkashin jagorancin Abdulsalami da Kukah ya damu matuka kan zaman lafiya da tsaro a jihohin, kuma ya bukaci ‘yan takarar su rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya.
Akwai fargaba dangane kan dalilin da suka sa ake ci gaba da samun tashe-tashen hankula a lokacin zabe a Nijeriya duk da kokarin da hukumoma da sauran masu ruwa da tsaki ke yi.

A saboda haka, kwamitin zaman lafiya na kasa ya ce ba zai karaya ba har sai halayen wasu ‘yan siyasa sun sauya a lokacin zabe, inda ya dage cewa zai yi kokarin ganin an gudanar da zaben cikin zaman lafiya bisa jajircewar ‘yan takarar gwamna da jam’iyyunsu da sauran masu ruwa da tsaki.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

A Jihar Imo
Da yake tofa albarkacin bakinsa, dan takarar gwamnan Jihar Imo a karkashin jam’iyyar PDP, Sanata Samuel Anyanwu, ya ce matakin da gwamnatin jihar take dauka na tunkarar kalubalen tsaro ne ke haddasa tashe-tashen hankula a jihar.

Anyanwu ya ce matasan jihar ba su da aikin yi, inda ya shawarci gwamnati da ta samar da ayyukan yi da gina masana’antu da samar da yanayin da zai taimaka wajen bunkasa kasuwanci.

A cewarsa, hakkin gwamnati ne ta kare rayuka da dukiyoyin al’umma, ya idan gwamnati ta kasa haka, za a kira ta da sunan wacce ta gaza.

A nasa bangaren, dan takarar gwamna na jam’iyyar LP, Sanata Athan Achonu ya kuma zargi gwamnatin jihar kan rashin tsaro a jihar.

‘Yan takarar sun nuna cewa a shirye suke su rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da kuma kudurin gudanar da zabe ba tare da tashin hankali ba.

Sai dai kuma, gwamnan jihar kuma dan takara a karkashin jam’iyyar APC, Hope Uzodimma y ace gwamnatinsa tana kokari wajen magance duk wani kalubalen da ka iya shafar zaben.

Kwamishiniyar zaben jihar, Farfesa Sylbia Agu ta bayyana cewa hukumar zaben ta yi isassun shirye-shirye tare da jami’an tsaro wajen kare ma’aikatanta.

A Jihar Kogi
A Jihar Kogi, dan takarar gwamna na jam’iyyar SDP, Murtala Ajaka, ya nuna sha’awarsa na sanya hannu kan duk wata yarjejeniyar zaman lafiya.

LEADERSHIP tuntubi mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben APC, Kingsley Fanwo da kuma babban mataimaki na musamman ga gwamnan Kogi kan harkokin yada labarai, Michael Ozigi, kan ko dan takararsu zai sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya, amma duk su biyun ba su amsa ba.

Haka shi ma, dan takarar jam’iyyar PDP, Dino Melaye bai amsa ba.

A Jihar Bayelsa
An kasa masun ‘yan takarar manyan jam’iyyun siyasa uku da mambobin majalisar yakin neman zabensu.

Hakan ya kasance ne sakamakon kara zafafa yakin neman zabe da jam’iyyu suke gudanarwa a dukkan kananan hukumomin jihar.

Dangane da matakan da hukumar zabe ke dauka na kare ma’aikatanta, shugaban sashen wayar da kan masu jefa kuri’a, Wilfred Ifogah, ya ce hukumar ta gudanar da tattaunawa da dama da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro a zaben.

Ya ce, “INEC ba ta aiki ita kadai ba. Akwai kwamitin tuntuba tsakanin hukumomin tsaro kan harkokin zabe (ICCES). Wannan tawaga ce ta dukkan hukumomin tsaro da ake da su a zaben jihar. Kwamishinan zabe da kwamishinan ‘yansanda ne ke jagorantar tawagar a kwacce jiha.”

A cewarsa, duk wannan na faruwa ne domin tabbatar da cewa masu kada kuri’a za su kasance a rumfunan zabe ba tare da wata matsala ba.

Tuni dai ake ci gaba da samun rashin tsaro a wadannan jihohi da za a gudanar da zaben gwamna.

Yayin da zaben Kogi zai iya samun cikas da ayyukan ‘yan daba kamar yadda aka gani a zaben da ya gabata, masu zabe a Imo da jami’an INEC na iya samun kalubalan ‘yan bindiga.

Har ila yau, a Jihar Bayelsa lamarin na matukar tayar da hankali, inda wasu ‘yan bindiga da ake zargin makiyaya ne ke kai hare-hare kan manoma da fararen hula har ma da jami’an tsaro.

Ita ma hukumar zabe na iya samu matsaloli wajen gudanar da zaben, wadanda suka shafi kan kayan aiki a lungu da sako na jihohin da saka sakamakon zabe ta na’ura da dai sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dino MelayeINECZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abun Da Ya Faru A MDD Gargadi Ne Ga Amurka

Next Post

Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 week ago
Kogi
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 week ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

1 week ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

2 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

2 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

2 weeks ago
Next Post
Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

LABARAI MASU NASABA

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

May 10, 2025
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

May 10, 2025
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

May 10, 2025
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

May 10, 2025
Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

May 10, 2025
Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

May 10, 2025
Kogi

ECOWAS Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Afrika Ta Yamma – Kwamred Bishir Dauda

May 10, 2025
Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.