ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Da Zaben Gwamnonin Imo, Kogi Da Bayelsa Ke Fuskanta

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Kogi

Kwanaki kadan ya rage a gudanar da zaben gwamna a jihohin Kogi, Imo da Bayelsa, sai dai akwai wasu kalubale da zabukan ka iya fuskanta, musamman na rashin tsaro da kaurace wa zaben da kuma yadda hukumar zabe mai zaman kanta za ta iya gudanar da sahihin zabe a daukacin jihohin ba tare da wata matsala ba.

Shi ya sa ma, tsohon shugaban kasa, Abdulsalami Abubakar da, Rabaran Mathew Hassan Kukah, sun yi kira ga daukacin ‘yan takara da magoya baya da su yi kokarin wajen gudanar da zabukan ba tare da tashe-tashen hankula ba.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da manyan ‘yan takarar gwamna a jihohin suke cacar baki tare da sukar juna, wanda hakan na iya haddasa tashe-tashen hankula a jihohinsu.

ADVERTISEMENT

A yayin da zaben gwamna a jihohin uku zai gudana a ranar 11 ga watan Nuwamba, 2023, kwamitin zaman lafiya na kasa karkashin jagorancin Abdulsalami da Kukah ya damu matuka kan zaman lafiya da tsaro a jihohin, kuma ya bukaci ‘yan takarar su rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya.
Akwai fargaba dangane kan dalilin da suka sa ake ci gaba da samun tashe-tashen hankula a lokacin zabe a Nijeriya duk da kokarin da hukumoma da sauran masu ruwa da tsaki ke yi.

A saboda haka, kwamitin zaman lafiya na kasa ya ce ba zai karaya ba har sai halayen wasu ‘yan siyasa sun sauya a lokacin zabe, inda ya dage cewa zai yi kokarin ganin an gudanar da zaben cikin zaman lafiya bisa jajircewar ‘yan takarar gwamna da jam’iyyunsu da sauran masu ruwa da tsaki.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

A Jihar Imo
Da yake tofa albarkacin bakinsa, dan takarar gwamnan Jihar Imo a karkashin jam’iyyar PDP, Sanata Samuel Anyanwu, ya ce matakin da gwamnatin jihar take dauka na tunkarar kalubalen tsaro ne ke haddasa tashe-tashen hankula a jihar.

Anyanwu ya ce matasan jihar ba su da aikin yi, inda ya shawarci gwamnati da ta samar da ayyukan yi da gina masana’antu da samar da yanayin da zai taimaka wajen bunkasa kasuwanci.

A cewarsa, hakkin gwamnati ne ta kare rayuka da dukiyoyin al’umma, ya idan gwamnati ta kasa haka, za a kira ta da sunan wacce ta gaza.

A nasa bangaren, dan takarar gwamna na jam’iyyar LP, Sanata Athan Achonu ya kuma zargi gwamnatin jihar kan rashin tsaro a jihar.

‘Yan takarar sun nuna cewa a shirye suke su rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da kuma kudurin gudanar da zabe ba tare da tashin hankali ba.

Sai dai kuma, gwamnan jihar kuma dan takara a karkashin jam’iyyar APC, Hope Uzodimma y ace gwamnatinsa tana kokari wajen magance duk wani kalubalen da ka iya shafar zaben.

Kwamishiniyar zaben jihar, Farfesa Sylbia Agu ta bayyana cewa hukumar zaben ta yi isassun shirye-shirye tare da jami’an tsaro wajen kare ma’aikatanta.

A Jihar Kogi
A Jihar Kogi, dan takarar gwamna na jam’iyyar SDP, Murtala Ajaka, ya nuna sha’awarsa na sanya hannu kan duk wata yarjejeniyar zaman lafiya.

LEADERSHIP tuntubi mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben APC, Kingsley Fanwo da kuma babban mataimaki na musamman ga gwamnan Kogi kan harkokin yada labarai, Michael Ozigi, kan ko dan takararsu zai sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya, amma duk su biyun ba su amsa ba.

Haka shi ma, dan takarar jam’iyyar PDP, Dino Melaye bai amsa ba.

A Jihar Bayelsa
An kasa masun ‘yan takarar manyan jam’iyyun siyasa uku da mambobin majalisar yakin neman zabensu.

Hakan ya kasance ne sakamakon kara zafafa yakin neman zabe da jam’iyyu suke gudanarwa a dukkan kananan hukumomin jihar.

Dangane da matakan da hukumar zabe ke dauka na kare ma’aikatanta, shugaban sashen wayar da kan masu jefa kuri’a, Wilfred Ifogah, ya ce hukumar ta gudanar da tattaunawa da dama da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro a zaben.

Ya ce, “INEC ba ta aiki ita kadai ba. Akwai kwamitin tuntuba tsakanin hukumomin tsaro kan harkokin zabe (ICCES). Wannan tawaga ce ta dukkan hukumomin tsaro da ake da su a zaben jihar. Kwamishinan zabe da kwamishinan ‘yansanda ne ke jagorantar tawagar a kwacce jiha.”

A cewarsa, duk wannan na faruwa ne domin tabbatar da cewa masu kada kuri’a za su kasance a rumfunan zabe ba tare da wata matsala ba.

Tuni dai ake ci gaba da samun rashin tsaro a wadannan jihohi da za a gudanar da zaben gwamna.

Yayin da zaben Kogi zai iya samun cikas da ayyukan ‘yan daba kamar yadda aka gani a zaben da ya gabata, masu zabe a Imo da jami’an INEC na iya samun kalubalan ‘yan bindiga.

Har ila yau, a Jihar Bayelsa lamarin na matukar tayar da hankali, inda wasu ‘yan bindiga da ake zargin makiyaya ne ke kai hare-hare kan manoma da fararen hula har ma da jami’an tsaro.

Ita ma hukumar zabe na iya samu matsaloli wajen gudanar da zaben, wadanda suka shafi kan kayan aiki a lungu da sako na jihohin da saka sakamakon zabe ta na’ura da dai sauransu.

Kogi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.