ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Da Zaben Gwamnonin Imo, Kogi Da Bayelsa Ke Fuskanta

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Kogi

Kwanaki kadan ya rage a gudanar da zaben gwamna a jihohin Kogi, Imo da Bayelsa, sai dai akwai wasu kalubale da zabukan ka iya fuskanta, musamman na rashin tsaro da kaurace wa zaben da kuma yadda hukumar zabe mai zaman kanta za ta iya gudanar da sahihin zabe a daukacin jihohin ba tare da wata matsala ba.

Shi ya sa ma, tsohon shugaban kasa, Abdulsalami Abubakar da, Rabaran Mathew Hassan Kukah, sun yi kira ga daukacin ‘yan takara da magoya baya da su yi kokarin wajen gudanar da zabukan ba tare da tashe-tashen hankula ba.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da manyan ‘yan takarar gwamna a jihohin suke cacar baki tare da sukar juna, wanda hakan na iya haddasa tashe-tashen hankula a jihohinsu.

ADVERTISEMENT

A yayin da zaben gwamna a jihohin uku zai gudana a ranar 11 ga watan Nuwamba, 2023, kwamitin zaman lafiya na kasa karkashin jagorancin Abdulsalami da Kukah ya damu matuka kan zaman lafiya da tsaro a jihohin, kuma ya bukaci ‘yan takarar su rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya.
Akwai fargaba dangane kan dalilin da suka sa ake ci gaba da samun tashe-tashen hankula a lokacin zabe a Nijeriya duk da kokarin da hukumoma da sauran masu ruwa da tsaki ke yi.

A saboda haka, kwamitin zaman lafiya na kasa ya ce ba zai karaya ba har sai halayen wasu ‘yan siyasa sun sauya a lokacin zabe, inda ya dage cewa zai yi kokarin ganin an gudanar da zaben cikin zaman lafiya bisa jajircewar ‘yan takarar gwamna da jam’iyyunsu da sauran masu ruwa da tsaki.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

A Jihar Imo
Da yake tofa albarkacin bakinsa, dan takarar gwamnan Jihar Imo a karkashin jam’iyyar PDP, Sanata Samuel Anyanwu, ya ce matakin da gwamnatin jihar take dauka na tunkarar kalubalen tsaro ne ke haddasa tashe-tashen hankula a jihar.

Anyanwu ya ce matasan jihar ba su da aikin yi, inda ya shawarci gwamnati da ta samar da ayyukan yi da gina masana’antu da samar da yanayin da zai taimaka wajen bunkasa kasuwanci.

A cewarsa, hakkin gwamnati ne ta kare rayuka da dukiyoyin al’umma, ya idan gwamnati ta kasa haka, za a kira ta da sunan wacce ta gaza.

A nasa bangaren, dan takarar gwamna na jam’iyyar LP, Sanata Athan Achonu ya kuma zargi gwamnatin jihar kan rashin tsaro a jihar.

‘Yan takarar sun nuna cewa a shirye suke su rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da kuma kudurin gudanar da zabe ba tare da tashin hankali ba.

Sai dai kuma, gwamnan jihar kuma dan takara a karkashin jam’iyyar APC, Hope Uzodimma y ace gwamnatinsa tana kokari wajen magance duk wani kalubalen da ka iya shafar zaben.

Kwamishiniyar zaben jihar, Farfesa Sylbia Agu ta bayyana cewa hukumar zaben ta yi isassun shirye-shirye tare da jami’an tsaro wajen kare ma’aikatanta.

A Jihar Kogi
A Jihar Kogi, dan takarar gwamna na jam’iyyar SDP, Murtala Ajaka, ya nuna sha’awarsa na sanya hannu kan duk wata yarjejeniyar zaman lafiya.

LEADERSHIP tuntubi mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben APC, Kingsley Fanwo da kuma babban mataimaki na musamman ga gwamnan Kogi kan harkokin yada labarai, Michael Ozigi, kan ko dan takararsu zai sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya, amma duk su biyun ba su amsa ba.

Haka shi ma, dan takarar jam’iyyar PDP, Dino Melaye bai amsa ba.

A Jihar Bayelsa
An kasa masun ‘yan takarar manyan jam’iyyun siyasa uku da mambobin majalisar yakin neman zabensu.

Hakan ya kasance ne sakamakon kara zafafa yakin neman zabe da jam’iyyu suke gudanarwa a dukkan kananan hukumomin jihar.

Dangane da matakan da hukumar zabe ke dauka na kare ma’aikatanta, shugaban sashen wayar da kan masu jefa kuri’a, Wilfred Ifogah, ya ce hukumar ta gudanar da tattaunawa da dama da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro a zaben.

Ya ce, “INEC ba ta aiki ita kadai ba. Akwai kwamitin tuntuba tsakanin hukumomin tsaro kan harkokin zabe (ICCES). Wannan tawaga ce ta dukkan hukumomin tsaro da ake da su a zaben jihar. Kwamishinan zabe da kwamishinan ‘yansanda ne ke jagorantar tawagar a kwacce jiha.”

A cewarsa, duk wannan na faruwa ne domin tabbatar da cewa masu kada kuri’a za su kasance a rumfunan zabe ba tare da wata matsala ba.

Tuni dai ake ci gaba da samun rashin tsaro a wadannan jihohi da za a gudanar da zaben gwamna.

Yayin da zaben Kogi zai iya samun cikas da ayyukan ‘yan daba kamar yadda aka gani a zaben da ya gabata, masu zabe a Imo da jami’an INEC na iya samun kalubalan ‘yan bindiga.

Har ila yau, a Jihar Bayelsa lamarin na matukar tayar da hankali, inda wasu ‘yan bindiga da ake zargin makiyaya ne ke kai hare-hare kan manoma da fararen hula har ma da jami’an tsaro.

Ita ma hukumar zabe na iya samu matsaloli wajen gudanar da zaben, wadanda suka shafi kan kayan aiki a lungu da sako na jihohin da saka sakamakon zabe ta na’ura da dai sauransu.

Kogi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.