• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Gwamnonin Da Suka Samu Nasara A Kotun Koli

by Bello Hamza, Abdullahi Muh'd Sheka, Hussein Yero and Khalid Idris Doya
2 years ago
in Rahotonni
0
Kalubalen Gwamnonin Da Suka Samu Nasara A Kotun Koli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

A ranar Jumma’a 12 ga watan Janairu 2024 ne kotun koli ta yanke hukuncin karshe a kan takaddamar da taso tun daga tokun sauraron kararrakin zaben gwamnoni a jihohin da suka hada da Legas, Kano, Bauchi, Filato da Zamfara inda kotun ta tabbatar da zaben da al’umma suka yi wa gwamnonin wadannan jihohin.

Ganin irin gwagwarmayar da aka yi fama da ita da yadda kan al’umma ya rarrabu, ya sa mutane da dama ke ganin akwai kalubalen da gwamnonin ke fuskanta a halin yanzu na hada kan al’umma ba tare da nuna bambancin siyasa ba.

  • Kasar Sin Ta Harba Kumbon Dakon Kaya Domin Aikewa Da Kayayyaki Ga Tashar Sararin Samaniya
  • ‘Yansanda Sun Cafke Wasu Mutane Biyu Da Ake Zargi Da Satar Keke-napep A Kano

Musamman a halin yanzu da ya kamata a fuskanci yi wa al’umma aiki, ganin mutane na fuskantar matsalolin tattalin arziki daban-daban da kuma matsaloilin tsaro da ke bukatar kulawa cikin gaggawa.

Kotun kolin ta yanke hukunci a kan zaben Babajide Sanwo-Olu na Legas, Abba Yusuf na Kano, Bala Mohammed na Bauchi, Caleb Mutfwang na Filato da kuma Dauda Lawal na Zamfara inda ta tabbatar da su a matsayin gwamnonin jihohinsu wanda hakan ya kawo karshen takaddamar da ke tattare da zaben gwamnonin da aka yi a shekarar 2023.

Kano

Batun Rusau Da Hada Kan Jam’iyya Ne A Kan Gaba

Akwai yiwuwar Gwamna Abba Kabir Yusuf zai fuskanci manyan kalubale da suka hada da rikicin cikin gida wanda tun kafin a ci Talata da Laraba aka fara jin karar tasowarsa, wadannan kuma ba ya rasa nasaba da yadda wasu daga cikin masu taimaka wa gwamnan da kuma wasu kwamishinonin suke karbar umrnin daga babbar fadar Jam’iyyar ta NNPP, domin kamar yadda aka sani Gwamana Abba kafin wannan lokaci, shi ne mai taimakawa na musamman (PA) na Sanata Kwankwaso, hakan ta sa wasu dagan cikin masu rike da manyan mukamai har yanzu suke masa kallon PA.

Hakazalika, akwai gagarumar matsalaar da ta kamata tun yanzu Gwamna Abba ya fara tunanin yadda zai magance ta rusau da aka yi wa ‘yan kasuwa da wasu daidaikun mutane a Birinin Kano.

Wannan ba karamin kalubale ba ne idan aka yi la’akari da kasancewar Kano cibiyar ciniki kuma ga shi kai tsaye ‘yan kasuwar aka fara tabawa. Sai kuma batun korar ma’aikata wadda a wata majiya ta shaida cewa wannan matsala ce da ta tayar da matukar kura da ake ganin ita ce ta kai wani babban jami’in gwamnatin tafiya jinya a asibiti, kodayake an sallamo shi.

Hakazalika, akwai batun masarautu hudu da tsohon Gwamna Ganduje ya kirkira, kuma ake ganin suna cikin abubuwan da ba su kwanta wa wannan gwamnati a zuciya ba, sannan suna da tsarin abubuwan da suka ambata a lokacin yakin neman zaben da dole su aiwatar da su, kamar batun kawar da gine-ginen da suka ce ba a yi su bisa ka’ida ba kuma suka yi masu dirar mikiya. Ko shakka babu akwai bukatar sabon gwamnan ya yi wa wannan matsala kallon tsanaki domin gudun sake fadawa wani rikicin.

Ganin yadda Kanawa suka nuna wa Gwamna Abba Kabir Yusuf kauna ya zama wajibi ya duba wasu daga cikin abubuwan da za su kara kyautata alakar gwmanatinsa da wasu sassan da suke ganin an saba masu a baya, kuma kamar yadda aka san al’adar siyasar Jihar Kano, akwai wasu rukunin al’umma kama da ga ‘yan Kasuwa, Malamai, iyayen kasa da masu fada aji daga cikin ‘yan siyasa da suke taka muhimmiyar rawa wajen nuna kyakkyawar alkiblar kowacce gwmanati, wannan tasa yake da muhimmacnin gaske gwamnan ya gaggauta yin la’akari da su domin taimaka wa gwamnatinsa. Duk da cewa dai jim kadan da yanke hukuncin kotun koli aka ji gwamnan ya sanar da kafa wani Kwamitin Dattijai da ya kunshi Tsoffin Gwmanonin Jihar Kano guda uku da suka hada da Malam Ibrahim Shekarau, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da kuma Dakta Abdullahi Umar Ganduje.

Zamfara

Mastalar Tsaro Da Bukatar Hada Kan Al’ummar Jihar

A yanzu haka hankalin Gwamna Dauda Lawal ya kwanta sakamakon tabbatar da shi da Babar Kotun Koli ta yi na cewa, shi ne zabben gwamna.

Daga kalubalen da Gwamna Dauda zai fuskanta, akwai daga bangaren ma’aikata,’yan siyasa da al’ummar gari-gari.

LEADERSHIP Hausa ta ji ra’yoyin mazauna Zamfara, kuma masana a kan zamantakeyar yadda Gwamna Dauda zai magance wadannan kalubalen da ke gabansa.

Kwamaret Ibrahim Kanoma Tsohon Ma’aikaci a Ma’aikatar yada labarai na Zamfara, ya bayyana cewa, babban kalubalen da ke gaban gwamna a bangaren ma’aikata shi ne dawo da darajar aikin.

Bangaren Siyasa kuma Malam Ibrahim Gada ya bayyana cewa, babban kalubalan Gwamna Dauda shi ne, Sanata Yari Abubakar, dan yadda a yanzu yake tafiyar da ‘yan siyasa da ba su tallafi da taimakonsu, lallai shi ma Gwamna Dauda sai ya kasance haka, tun da ga aiki yana ta zubawa sai kuma alheri ga ‘yan siyasa don yadda ake cikin yanayi a yanzu haka duk ayyukan da Gwamna Dauda zai yi idan bai hada da tallafin kudi da abinci ba lallai akwai matsala.

Don haka Gwamna Dauda ya duba da kyau ya bullo da wasu shiri na ba da tallafi ga al’umma don rage radadin halin da ake ciki, in ji shi.

Filato

Matsalar Tsaro Ita Ce Babbar Kalubalen Da Gwamnan Jihar Ke Fuskanta

Bayan tabbatar da Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, a matsayin gwamnan jihar ba kamar yadda kotun daukaka karar ta yi na dora dan takarar jam’iyyar APC, Nentawe Goshwe ba, babban kalubalen da yake fuskanta shi ne rashin tsaro wanda hare-haren da aka kai wa wasu al’ummomi lokacin bukukuwan kirsemeti suka fayyace irin matsalar tsaron da jihar ke ciki.

Baya ga sha’anin tsaro, ta fuskar siyasa ma Gwamna Caleb na fuskantar kalubalen hada kai da ‘yan majalisa da suka fito daga jihar wadanda suka fi yawa a jam’iyyar dawa ta APC a jihar. Dole Gwamnan ya samar da hanyoyin kara fahimtar juna da mutunta juna a tsakanin al’ummar jihar in har ana son samun ci gaba mai dorewa ci gaba da zamantakewa a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Sa Ranar Sauraron Tuhumar Da Ake Wa Manchester United

Next Post

Manzon Musamman Na Shugaba Xi Jinping Na Kasar Sin Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Liberia

Related

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

2 weeks ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

2 weeks ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

3 weeks ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

3 weeks ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

4 weeks ago
Next Post
Manzon Musamman Na Shugaba Xi Jinping Na Kasar Sin Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Liberia

Manzon Musamman Na Shugaba Xi Jinping Na Kasar Sin Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Liberia

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun DaÆ™ile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

Jami’an Tsaro Sun DaÆ™ile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

August 7, 2025
An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

August 7, 2025
Jama’a Suke Tona Asirin GurÉ“atattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

Jama’a Suke Tona Asirin GurÉ“atattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

August 7, 2025
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.