• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanin Turkiyya Ya Fara Aikin inganta Noman Zamani A Zamfara 

by Leadership Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Kamfanin Turkiyya Ya Fara Aikin inganta Noman Zamani A Zamfara 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani fitaccen kamfanin ƙasar Turkiyya mai suna Direkci zai fara aikin samar da na’urorin zamani a harkar noma tare da samar da lambunan zamani domin bunƙasa noma a Jihar Zamfara.

 

A ranar Asabar ɗin da ta gabata ne, Nurullah Mehmet, Manajan Darakta kuma Babban Jami’in Gudanarwa na cibiyar Direkci, ya jagoranci tawagar da suka kai wa Gwamna Dauda Lawal ziyarar aiki a ofishinsa a gidan gwamnati da ke Gusau.

  • Babu Uziri A Yaki Da Cin Zarafin Mata – Mohamed M. Fall
  • Shettima Ya Yaba Wa BUK Kan Bai Wa Dalibai Guraben Karatu Cikin Adalci

Kamfanin na ƙasar Turkiyya na shirin kawo sauyi a harkar noma a Jihar Zamfara ta hanyar noman auduga, da raƙe, da waken soya mai tarin yawa.

 

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Baya ga noman gargajiya, cibiyar za ta bullo da hanyoyin noma na zamani, gami da amfani da fasaha wajen samar da lambuna da kiwon kaji, waɗanda za su ƙara inganta fannoni da dama a jihar.

 

A nasa jawabin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatin sa na tabbatar da samar da abinci da samar da ayyukan yi ga al’ummar Jihar Zamfara.

 

“Kamar yadda na yi alƙawari a lokacin yaƙin neman zabe, idan aka zabe ni, gwamnatina za ta mai da hankali kan tsaro, noma da samar da abinci, ilimi, kiwon lafiya, tattalin arziki, da ƙarfafawa al’umma.

 

“An san al’ummarmu a jihar Zamfara da noma. Burin mu shi ne mu farfaɗo da wannan fanni. Muna da burin tabbatar da tsaron jihar domin mutane su koma gonakinsu.

 

“Abu mai muhimmanci shi ne, bayan tabbatar da tsaro a gonaki, mataki na gaba shi ne samar da na’urorin zamani ga manoman mu, kasancewar mun riga mun sami filaye da ma’aikata.

 

“Wannan shi ne dalilin da ya sa muke maraba da haɗin gwiwar masu zuba jari irin su Direkci.

 

“Na yi tafiya zuwa Turkiyya a watan Yuli, inda na ziyarci ayyukan gonaki, kiwo, ayyukan kiwon kaji, da kuma masana’antar sarrafa na’urorin ayyukan noma ta Turk. Cibiyar Direkci ta zo Zamfara ne domin bullo da ci gaban fasaha a harkar noma.”

 

A farko, Nurullah Mehmet, Manajan Darakta kuma Babban Jami’in Gudanarwa na Direkci, ya yaba wa Gwamna Lawal bisa ɗimbin ayyukan da gwamnatinsa ta fara a cikin ƙanƙanin lokaci.

 

“Kamfanin mu Direkci yana gudanar da ayyuka da dama a jihohi daban-daban na Nijeriya.

 

“Shirin noma na Direkci a jihar Zamfara zai inganta darajar noma tare da jawo zuba jari, da bunƙasa tattalin arzikin cikin gida.

 

“Shigo da lambunan zamani zai habaka noma a duk shekara, wajen kare amfani gona daga fari da sauran abubuwa.

 

“Noman zamani da na kiwon kaji za su samar da guraben aikin yi a matakai daban-daban, daga ma’aikatan gona zuwa ƙwararru a harkar noma.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dokar Haraji: Ƙarawa Masu Kudi Haraji Ba Talakawa Ba Shi Ya Kamata

Next Post

Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi Jami’anta Kan Rubutu A Kafafen Sadarwa 

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

7 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

8 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

11 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

13 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

16 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

17 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi Jami’anta Kan Rubutu A Kafafen Sadarwa 

Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi Jami'anta Kan Rubutu A Kafafen Sadarwa 

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.