Assalamu alaikum warahmatullah wabarkatuhu ‘yan uwa masu albarka,da fatan muna lafiya maraba da wadannan kwanaki masu albarka, muna rokon Allah SWT Ya sa mu dace da falalarsu, ya sa muna cikin masu azumtan Arfat ya sa mu ga ranar Sallah cikin lafiya imani da rufin asiri.
‘Yar uwa mai albarka ga Sallar layya ta zo, kuma muna sane da yanayin da muke ciki a wannan rayuwar, don haka ki yi hakuri idan mijinki ba shi da karfin yi muku yanka, kar ki ga gazawarsa, abin yanka yanzu ba kowa zai iya ba sai wanda Allah ya hore wa.
- Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
- Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya
Wannan mijin naki da yake kokarin kawo miki abinci amma bai samu damar da zai sayi abin layya ba, da yawan mata na nan abincin ma ba su da shi, don Allah ki yi hakuri kin ji, mijin ki ba zai so a ce yau Sallah guda amma ba abin yanka a gidansa ba sai dole.
Idan Allah ya hore miki ke za ki iya yanka don Allah kar ki yi wa kan ki da ‘ya’yanki da mijinki rowa, zaman aure rufin asiri ake so a cikin sa, don haka ki sayi abin da ya sauwaka ki yanka ku yi amfani da shi wannan ma babbar ni’ima ce tun da shi bashi da shi ke kuma Allah ya baki.
Ga matan da Allah bai hore musu ba kuma mazajen su ma basu da shi, don Allah ku yi hakuri, ku mika kukanku ga Allah in sha Allah zai kawo mafita ta inda ba ki yi zato ba bi’izinillah.
Ya ke ‘yar uwa mai albarka,idan kina da ‘ya a gidan aure ko kanwa,don Allah mu tuntube su ranar Sallah mu ji halin da suke ciki su da jikokinki, wannan lokaci ne da za ki taimaka musu don ganin farin cikin su, abin akwai wahala a Sallah ka ji gida shiru ba labari, don Allah iyaye a taimaka ma yaran da suke gidan aure.
Sannan makota masu karfi ku duba girman Allah ku yi sadaka idan kun yi yanka, ana raba naman Sallah uku, na amfanin gida, sadaka ma mabukata da kuma na kyauta ma, ‘yan uwa da abokan arziki, hakan zai taimaka wajen kowa ya yi walwala ya san Sallah ake yi.
Shekarar da ta wuce wata ke ba da labari ta ce, “Shekarun da suka wuce makotanta shanu biyu suka yanka da raguna wanda suke kallon juna, dayan makwabtan kuma shanu da raguna, amma ba wanda ya aiko musu sadaka ga yara ta kulle su a gida ta hana kowa fita, Jama’a wannan wane irin makotaka ne Sallah guda. Allah ya sa mu gane.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp