ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

by Bilkisu Tijjani and Sulaiman
12 months ago
aure

Assalamu alaikum warahmatullah wabarkatuhu ‘yan uwa masu albarka,da fatan muna lafiya maraba da wadannan kwanaki masu albarka, muna rokon Allah SWT Ya sa mu dace da falalarsu, ya sa muna cikin masu azumtan Arfat ya sa mu ga ranar Sallah cikin lafiya imani da rufin asiri.

‘Yar uwa mai albarka ga Sallar layya ta zo, kuma muna sane da yanayin da muke ciki a wannan rayuwar, don haka ki yi hakuri idan mijinki ba shi da karfin yi muku yanka, kar ki ga gazawarsa, abin yanka yanzu ba kowa zai iya ba sai wanda Allah ya hore wa.

  • Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
  • Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Wannan mijin naki da yake kokarin kawo miki abinci amma bai samu damar da zai sayi abin layya ba, da yawan mata na nan abincin ma ba su da shi, don Allah ki yi hakuri kin ji, mijin ki ba zai so a ce yau Sallah guda amma ba abin yanka a gidansa ba sai dole.

ADVERTISEMENT

Idan Allah ya hore miki ke za ki iya yanka don Allah kar ki yi wa kan ki da ‘ya’yanki da mijinki rowa, zaman aure rufin asiri ake so a cikin sa, don haka ki sayi abin da ya sauwaka ki yanka ku yi amfani da shi wannan ma babbar ni’ima ce tun da shi bashi da shi ke kuma Allah ya baki.

Ga matan da Allah bai hore musu ba kuma mazajen su ma basu da shi, don Allah ku yi hakuri, ku mika kukanku ga Allah in sha Allah zai kawo mafita ta inda ba ki yi zato ba bi’izinillah.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki

Ya ke ‘yar uwa mai albarka,idan kina da ‘ya a gidan aure ko kanwa,don Allah mu tuntube su ranar Sallah mu ji halin da suke ciki su da jikokinki, wannan lokaci ne da za ki taimaka musu don ganin farin cikin su, abin akwai wahala a Sallah ka ji gida shiru ba labari, don Allah iyaye a taimaka ma yaran da suke gidan aure.

Sannan makota masu karfi ku duba girman Allah ku yi sadaka idan kun yi yanka, ana raba naman Sallah uku, na amfanin gida, sadaka ma mabukata da kuma na kyauta ma, ‘yan uwa da abokan arziki, hakan zai taimaka wajen kowa ya yi walwala ya san Sallah ake yi.

Shekarar da ta wuce wata ke ba da labari ta ce, “Shekarun da suka wuce makotanta shanu biyu suka yanka da raguna wanda suke kallon juna, dayan makwabtan kuma shanu da raguna, amma ba wanda ya aiko musu sadaka ga yara ta kulle su a gida ta hana kowa fita, Jama’a wannan wane irin makotaka ne Sallah guda. Allah ya sa mu gane.

Naman Sallah
Bilkisu Tijjani
+ posts Bio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?
Naman Sallah
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
Uwargida Sarautar Mata

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

May 30, 2026
Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
Uwargida Sarautar Mata

Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki

May 24, 2026
aure
Uwargida Sarautar Mata

Kuskure Goma (10) Da Matan Aure Ke Yi A Gidan Miji

May 16, 2026
Next Post
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al'umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.