• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Abinci Na Kara Ta’azzara A Nijeriya

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Karancin Abinci Na Kara Ta’azzara A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matsalar karancin abinci a Nijeriya, na kara ci gaba da ta’azzara kamar yadda wasu manoma a kasar suka bayyana; inda suka ce, ana ci gaba da samun raguwar amfanin gona, sakamakon matsalar afkuwar iftila’in ambaliyar ruwan sama da sauyin yanayi da kalubalen rashin tsaro da kuma faduwar darajar Naira.

Haka zalika, shashen samar da abinci na Gwamnatin Kasar Amurka (USDA), ya yi hasashen cewa; za a samu raguwar noman Shinkafa, Gero, Rogo, Masara da kuma Waken Soya a wannan shekara 2024 a Nijeriya.

  • Masu Masana’antu Na Kasar Sin Sun Raba Fasahohinsu A Majalisar Dinkin Duniya
  • An Samu Sabuwar Damar Kyautata Hulda Tsakanin Sin Da Hungary

Koda-yake, wasu alkaluma sun bayyana cewa; Nijeriya ta kasance kan gaba a fadin duniya, wajen noma amfanin gonan da suka hada da Masara da Rogo.

Wasu jami’ai, a Ma’aikatar Aikin Noma ta Tarayya ta shaida wa LEADERSHIP cewa, ta samu madafar bayani kan matsayin amfanin da ake nomawa a kasar nan.

Har ila yau, duk da samun karin yawan manoma da aka yi a fadin wannan kasa, wasu manyan amfanin gonar za su fuskanci matsala; sakamakon faduwar darajar Naira, wanda hakan zai jawo raguwar noma a shekarar 2024.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

Sai dai a 2022, alkaluma sun nuna cewa; an samu karin masu yin noma da kashi 119.9, duk da dimbin kalubalen da manoman kasar ke fuskanta.

Kididdiga ta baya-bayan nan, ciki har da wadda aka samo daga (USDA), sun yi hasashen cewa; an samu ruguwar noman Shinkafa a Nijeriya da tan miliyan 5.355 daga 2022 zuwa 2023 tare kuma da kara samun raguwar noman nata da tan miliyan 5.229 daga 2023 zuwa 20 24.

Haka zalika, an samu raguwar noman Masara da tan miliyan 12.75 a shekarar 2021, wadda ta kai kashi 8 cikin 100; sai kuma kara samun raguwar noman nata da tan miliyan 11 daga 2024 zuwa 2025.

Kazalika, an kuma samun raguwar noman Dawa da tan miliyan 6.742 daga 2022 zuwa 20 23, inda kuma za a kara samun raguwar noman Dawar da tan miliyan 6, 700 daga 2023 zuwa 2024.

Sashen samar da abinci na Majalisar Dinkin Duniya (FAO), ya yi hasashen cewa, ‘yan Nijeriya sama da miliyan 31.5; za su fuskanci karancin abinci daga watan Yuni zuwa na Agustan 2024.

Wani rahoto da Hukumar Samar da Abinci ta ‘Cadre Harmonise’ ta fitar ya nuna cewa, a watan Maris da ya gabata; Nijeriya ta fuskanci babban kalubalen rashin tsaro, wanda hakan ya jawo tsaiko wajen aiwatar noma.

Bugu da kari, a yayin da ake shirin fara yin noma gadan-gadan a wannan damina ta bana, an yi hasashen za a samu koma-baya ta fannin noma kwarai da gaske, musamman duba da yadda kalubalen rashin tsaro ke neman gagarar Kundila.

Shugaban Kungiyar Manoma ta Kasa (AFAN), Arc. Kabir Ibrahim; a hirarsa da LEADERSHIP, ya bayyana wasu daga cikin kalubalen da fannin aikin na noma a wannan kasa ke ci gaba da fuskanta, kamar kalubalen rashin tsaro, rashin samun kayan aikin noma na zamani, ambaliyar ruwan sama da kuma tsadar kudin da ake biyan leburorin da suke aiki.

Haka zalika, a Jihar Kwara noman Shinkafa, Masara, Gyada, Doya, Dawa, Wake da sauran amfanin gona ya yi matukar raguwa a lokacin noman rani da na damina daga shekarar 2022 zuwa 2023, inda wasu manoma a jihar suka sheda wa jaridar LEADERSHIP cewa, hakan ya faru ne sakamakon rashin samun dauki daga gwamnatin tarayya da kuma ta jihar.

Haka nan,  a Jihar Biniwe noman Gero, Wake, Masara, Rogo, Gyada, Dawa da kuma Doya ya yi matukar raguwa a shekarar 2022, musamman saboda harin da wasu Fulani suka kai wa yankunan da ake yin noman, kazalika ambaliyar ruwan sama da kuma hare-haren ‘yan bindiga, wanda ya tarwatsa dimbin manoma daga matsugunansu.

Har wa yau, wasu manoma a Jihar Filato; kalubalen samun hare-haren ‘yan bindiga, musamman wanda aka kai a ranar 24 ga watan Disambar 2023, a Kananan Hukumomin Mangu da Bokkos; ya jawo wa manoma tabka asara.

A Jihar Bayelsa kuwa, matsalar kwarar danyen mai; ita ce babbar matsalar da manoma da gonakinsu ke fuskanta, musamman manoman Shinkafa.

Sai dai, wani manomin Shinkafa a yankin Akassa na Karamar Hukumar Brass a jihar, Mista Inatimi Peter Odio ya sheda wa LEADERSHIP Hausa cewa, matsalar kwarar danyen mai ya ragu; sakamakon kokarin da jami’an tsaron sintiri na Tantita suka yi a shekarar 2022, wanda hakan ya bai wa manoma damar noman Shinkafa.

Haka labarin ma yake a Jihar Neja, inda noman Doya da na Masara ya ragu sakamakon hare-haren ‘yan bindiga a kan manoma, domin kuwa har a yanzu wasu gonaki a yankunan Shiroro, Munya, Rafi, Mariga, Rijau da kuma wasu sassan Karamar Hukumar Paikoro da aka noma wadannan amfanin gona ke fuskantar hare-haren ‘yan bindiga, wanda hakan ya tilasta wa manoma a wadannan gurare yin watsi da noman tare da yin kaura daga yankunan nasu, inda a yanzu suke zaune a sansanin ‘yan gudun hijira a jihar.

Haka zalika, mai yiwuwa lamarin ba zai sauya akalar noman bana ba, duda da yadda maharan ke ci gaba da kai hare-hare kauyuka da dama na jihar.

Wannan batu haka yake a Jihar Osun ma, duba da yadda yawan Fulani Makiyaya ke yin kuste a gonakin manoma tare da satar amfanin gona, sannan kuma da yadda jihar ta fuskanci matsalar yin noma a kakar noma biyu.

Haka nan a Jihar Abiya, inda aka fara samun koma bayan a bangaren noma tun daga shekarar 2022, inda aka danganta matsalar kan amfani da kayan noma na gargajiya tare da rashin samar da ingantaccen Irin noma da tsadar kayan aikin noman da rashin samun goyon baya daga wurin gwamnatin jihar da rashin samar da rumbunan zamani na adana amfanin da aka noma da rashin samar da tituna don jigilar amfanin gonar da sace amfanin gonar da kuma hare-haren Fulani Makiyaya da sauran makamantansu.

A Jihar Ekiti kuwa, wani manomi Mista Olajide Olagunju ya ce, a watan Yunin 2022, noman Masara, Rogo da Doya ya yi matukar raguwa a jihar, sakamakon wasu matsaloli da suka hada da cututtukan da ke harbin amfanin gona da rashin samar da rumbuna na zamani wadanda za a adana amfanin gonar da aka noma, rashin samun takin zamani, gazawar samun rancen kudi daga bankuna, rashin samun saukar ruwa sama da wuri da sauransu.

A Jihar Sokoto kuma, shekaru biyu da suka gabata; noman Shinkafa, Gero, Masara, Rogo, Gyada, Doya da kuma Dawa ya yi matukar raguwa, sakamakon hare-haren ‘yan bindiga a wasu yankunan jihar.

Har ila yau, ita ma Jihar Kaduna ba ta tsira daga wannan matsala ba, domin kuwa wasu daga cikin manoman jihar sun danganta hakan da karuwar hare-haren ‘yan bindiga a wasu yankuna na jihar da kuma karancin kudi da wasu manoma ke fuskanta na kara noman Masara da Gero, domin ci da kuma sayarwa.

Wani manomin Masara; Gideon Cyprian, ya sheda wa LEADERSHIP Hausa cewa, hare-haren ‘yan bindiga ya yi matukar jawo koma-baya ga aikin noma a 2022, inda ya ce; a shekarar baya, ya girbe buhu takwas na Masara a wani kauye da ke jihar, amma sakamakon wannan hare-hare na ‘yan bindiga, yanzu ba  ya iya zuwa gonar da ya karbi haya a wannan kauye, don gudanar da wannan aiki na noma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Karancin AbinciTa'azzara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin Microsoft Ya Kori Ma’aikata A Cibiyar Raya Afrika

Next Post

Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – Inuwa

Related

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

3 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

3 days ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

4 days ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

5 days ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 weeks ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

2 weeks ago
Next Post
Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – Inuwa

Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya - Inuwa

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno

June 25, 2025
Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

June 25, 2025
Sojoji

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

June 25, 2025
Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

June 25, 2025
Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

June 25, 2025
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

June 25, 2025
Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

June 25, 2025
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

June 25, 2025
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.