• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Kudi Ba Zai Shafi Zaben 2023 Ba —INEC 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Karancin Kudi Ba Zai Shafi Zaben 2023 Ba —INEC 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya ce karancin kudi da ake fama da shi ba zai shafi zaben ranar 25 ga watan Fabrairu da na ranar 11 ga Maris da za a yi ba.

Yakubu ya bayyana haka ne don kawar da damuwar da ake fama da ita na karancin Naira gabanin zaben a ranar Asabar.

  • Abin Da Ya Sa Manoma Suka Ki Sayar Wa Da ‘Yan  Kasuwa Amfanin Gonakansu
  • Ina Amfani Da Whatapps, Facebook Da Tiktok Wajen Tallata Kasuwancina

Ya shaida haka ne a Abuja bayan ya ziyarci cibiyar horas da ma’aikatan wucin gadi.

An dai shiga fargabar cewa za a iya dage babban zaben kasar nan na bana ko kuma a samu kura-kurai sakamakon matsalar kudi da ake fuskanta biyo bayan canjin kudi da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya yi.

Idan dai ba a manta ba a kwanakin baya, Farfesa Yakubu ya jagoranci tawagar gudanarwar hukumar zuwa hedikwatar CBN, inda gwamnan CBN, Mista Godwin Emefiele, ya tabbatar wa hukumar da kudaden da ake bukata domin gudanar da zaben.

Labarai Masu Nasaba

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

“Mun ziyarci CBN a makon da ya gabata kan batun tsabar kudi domin biyan wasu ayyuka da za mu yi a ranar zabe.

“Yawancin biyan kudi da na kayayyakin ayyuka an yi shi ne ta Intanet.

“Amma akwai wasu ayyuka masu mahimmanci wadanda za a biya da tsabar kudi; kuma shi ya sa muka je CBN kuma kadan ne na kasafin kudin.

“Babban bankin kasar nan ya tabbatar mana da cewa ba za mu fuskanci wani tsaiko ba dangane da hakan. Don haka babu wata matsala dangane da hakan,” in ji shi.

Shugaban na INEC ya bayyana cewa hukumar ta shirya tsaf domin gudanar da zabukan shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya a ranar Asabar 25 ga Fabrairu, 2023.

Yakubu, wanda ya bayyana jin dadinsa da ci gaban da aka samu kawo yanzu, ya ba da tabbacin cewa a wannan lokaci a mako mai zuwa, ‘yan Nijeriya za su kada kuri’a a rumfunan zabe sama da 176,000 domin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya.

Ya kuma ce za a kuma bayyana zabin da ‘yan Nijeriya suka yi na zaben shugaban kasa a Abuja.

Dangane da halin da ake ciki na tsaro a kasar nan, ya ce zanga-zangar da ake yi kan karancin kudi lamari ne na tsaro, wanda za a tattauna da hukumomin tsaro.

Ya ce jami’an tsaro sun bai wa hukumar tabbacin shirinsu na tabbatar da tsaro a duk fadin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECKarancin KudiTsaroZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abin Da Ya Sa Manoma Suka Ki Sayar Wa Da ‘Yan  Kasuwa Amfanin Gonakansu

Next Post

Tsarin Sauyin Kudi Ya Taimaka Wa ‘Yan Kasa Wajen Zama Cikin Aminci – CIS Sunday,

Related

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

3 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

4 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

18 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

21 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

1 day ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

1 day ago
Next Post
Tsarin Sauyin Kudi Ya Taimaka Wa ‘Yan Kasa Wajen Zama Cikin Aminci – CIS Sunday,

Tsarin Sauyin Kudi Ya Taimaka Wa ‘Yan Kasa Wajen Zama Cikin Aminci - CIS Sunday,

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.