ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Kudi Ba Zai Shafi Zaben 2023 Ba —INEC 

by Sadiq
3 years ago
INEC

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya ce karancin kudi da ake fama da shi ba zai shafi zaben ranar 25 ga watan Fabrairu da na ranar 11 ga Maris da za a yi ba.

Yakubu ya bayyana haka ne don kawar da damuwar da ake fama da ita na karancin Naira gabanin zaben a ranar Asabar.

  • Abin Da Ya Sa Manoma Suka Ki Sayar Wa Da ‘Yan  Kasuwa Amfanin Gonakansu
  • Ina Amfani Da Whatapps, Facebook Da Tiktok Wajen Tallata Kasuwancina

Ya shaida haka ne a Abuja bayan ya ziyarci cibiyar horas da ma’aikatan wucin gadi.

ADVERTISEMENT

An dai shiga fargabar cewa za a iya dage babban zaben kasar nan na bana ko kuma a samu kura-kurai sakamakon matsalar kudi da ake fuskanta biyo bayan canjin kudi da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya yi.

Idan dai ba a manta ba a kwanakin baya, Farfesa Yakubu ya jagoranci tawagar gudanarwar hukumar zuwa hedikwatar CBN, inda gwamnan CBN, Mista Godwin Emefiele, ya tabbatar wa hukumar da kudaden da ake bukata domin gudanar da zaben.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

“Mun ziyarci CBN a makon da ya gabata kan batun tsabar kudi domin biyan wasu ayyuka da za mu yi a ranar zabe.

“Yawancin biyan kudi da na kayayyakin ayyuka an yi shi ne ta Intanet.

“Amma akwai wasu ayyuka masu mahimmanci wadanda za a biya da tsabar kudi; kuma shi ya sa muka je CBN kuma kadan ne na kasafin kudin.

“Babban bankin kasar nan ya tabbatar mana da cewa ba za mu fuskanci wani tsaiko ba dangane da hakan. Don haka babu wata matsala dangane da hakan,” in ji shi.

Shugaban na INEC ya bayyana cewa hukumar ta shirya tsaf domin gudanar da zabukan shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya a ranar Asabar 25 ga Fabrairu, 2023.

Yakubu, wanda ya bayyana jin dadinsa da ci gaban da aka samu kawo yanzu, ya ba da tabbacin cewa a wannan lokaci a mako mai zuwa, ‘yan Nijeriya za su kada kuri’a a rumfunan zabe sama da 176,000 domin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya.

Ya kuma ce za a kuma bayyana zabin da ‘yan Nijeriya suka yi na zaben shugaban kasa a Abuja.

Dangane da halin da ake ciki na tsaro a kasar nan, ya ce zanga-zangar da ake yi kan karancin kudi lamari ne na tsaro, wanda za a tattauna da hukumomin tsaro.

Ya ce jami’an tsaro sun bai wa hukumar tabbacin shirinsu na tabbatar da tsaro a duk fadin kasar nan.

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Tsarin Sauyin Kudi Ya Taimaka Wa ‘Yan Kasa Wajen Zama Cikin Aminci – CIS Sunday,

Tsarin Sauyin Kudi Ya Taimaka Wa ‘Yan Kasa Wajen Zama Cikin Aminci - CIS Sunday,

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.