ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Kudi Ba Zai Shafi Zaben 2023 Ba —INEC 

by Sadiq
3 years ago
INEC

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya ce karancin kudi da ake fama da shi ba zai shafi zaben ranar 25 ga watan Fabrairu da na ranar 11 ga Maris da za a yi ba.

Yakubu ya bayyana haka ne don kawar da damuwar da ake fama da ita na karancin Naira gabanin zaben a ranar Asabar.

  • Abin Da Ya Sa Manoma Suka Ki Sayar Wa Da ‘Yan  Kasuwa Amfanin Gonakansu
  • Ina Amfani Da Whatapps, Facebook Da Tiktok Wajen Tallata Kasuwancina

Ya shaida haka ne a Abuja bayan ya ziyarci cibiyar horas da ma’aikatan wucin gadi.

ADVERTISEMENT

An dai shiga fargabar cewa za a iya dage babban zaben kasar nan na bana ko kuma a samu kura-kurai sakamakon matsalar kudi da ake fuskanta biyo bayan canjin kudi da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya yi.

Idan dai ba a manta ba a kwanakin baya, Farfesa Yakubu ya jagoranci tawagar gudanarwar hukumar zuwa hedikwatar CBN, inda gwamnan CBN, Mista Godwin Emefiele, ya tabbatar wa hukumar da kudaden da ake bukata domin gudanar da zaben.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

“Mun ziyarci CBN a makon da ya gabata kan batun tsabar kudi domin biyan wasu ayyuka da za mu yi a ranar zabe.

“Yawancin biyan kudi da na kayayyakin ayyuka an yi shi ne ta Intanet.

“Amma akwai wasu ayyuka masu mahimmanci wadanda za a biya da tsabar kudi; kuma shi ya sa muka je CBN kuma kadan ne na kasafin kudin.

“Babban bankin kasar nan ya tabbatar mana da cewa ba za mu fuskanci wani tsaiko ba dangane da hakan. Don haka babu wata matsala dangane da hakan,” in ji shi.

Shugaban na INEC ya bayyana cewa hukumar ta shirya tsaf domin gudanar da zabukan shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya a ranar Asabar 25 ga Fabrairu, 2023.

Yakubu, wanda ya bayyana jin dadinsa da ci gaban da aka samu kawo yanzu, ya ba da tabbacin cewa a wannan lokaci a mako mai zuwa, ‘yan Nijeriya za su kada kuri’a a rumfunan zabe sama da 176,000 domin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya.

Ya kuma ce za a kuma bayyana zabin da ‘yan Nijeriya suka yi na zaben shugaban kasa a Abuja.

Dangane da halin da ake ciki na tsaro a kasar nan, ya ce zanga-zangar da ake yi kan karancin kudi lamari ne na tsaro, wanda za a tattauna da hukumomin tsaro.

Ya ce jami’an tsaro sun bai wa hukumar tabbacin shirinsu na tabbatar da tsaro a duk fadin kasar nan.

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Tsarin Sauyin Kudi Ya Taimaka Wa ‘Yan Kasa Wajen Zama Cikin Aminci – CIS Sunday,

Tsarin Sauyin Kudi Ya Taimaka Wa ‘Yan Kasa Wajen Zama Cikin Aminci - CIS Sunday,

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.