ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karancin Kudi Ba Zai Shafi Zaben 2023 Ba —INEC 

by Sadiq
3 years ago
INEC

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya ce karancin kudi da ake fama da shi ba zai shafi zaben ranar 25 ga watan Fabrairu da na ranar 11 ga Maris da za a yi ba.

Yakubu ya bayyana haka ne don kawar da damuwar da ake fama da ita na karancin Naira gabanin zaben a ranar Asabar.

  • Abin Da Ya Sa Manoma Suka Ki Sayar Wa Da ‘Yan  Kasuwa Amfanin Gonakansu
  • Ina Amfani Da Whatapps, Facebook Da Tiktok Wajen Tallata Kasuwancina

Ya shaida haka ne a Abuja bayan ya ziyarci cibiyar horas da ma’aikatan wucin gadi.

ADVERTISEMENT

An dai shiga fargabar cewa za a iya dage babban zaben kasar nan na bana ko kuma a samu kura-kurai sakamakon matsalar kudi da ake fuskanta biyo bayan canjin kudi da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya yi.

Idan dai ba a manta ba a kwanakin baya, Farfesa Yakubu ya jagoranci tawagar gudanarwar hukumar zuwa hedikwatar CBN, inda gwamnan CBN, Mista Godwin Emefiele, ya tabbatar wa hukumar da kudaden da ake bukata domin gudanar da zaben.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

“Mun ziyarci CBN a makon da ya gabata kan batun tsabar kudi domin biyan wasu ayyuka da za mu yi a ranar zabe.

“Yawancin biyan kudi da na kayayyakin ayyuka an yi shi ne ta Intanet.

“Amma akwai wasu ayyuka masu mahimmanci wadanda za a biya da tsabar kudi; kuma shi ya sa muka je CBN kuma kadan ne na kasafin kudin.

“Babban bankin kasar nan ya tabbatar mana da cewa ba za mu fuskanci wani tsaiko ba dangane da hakan. Don haka babu wata matsala dangane da hakan,” in ji shi.

Shugaban na INEC ya bayyana cewa hukumar ta shirya tsaf domin gudanar da zabukan shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya a ranar Asabar 25 ga Fabrairu, 2023.

Yakubu, wanda ya bayyana jin dadinsa da ci gaban da aka samu kawo yanzu, ya ba da tabbacin cewa a wannan lokaci a mako mai zuwa, ‘yan Nijeriya za su kada kuri’a a rumfunan zabe sama da 176,000 domin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya.

Ya kuma ce za a kuma bayyana zabin da ‘yan Nijeriya suka yi na zaben shugaban kasa a Abuja.

Dangane da halin da ake ciki na tsaro a kasar nan, ya ce zanga-zangar da ake yi kan karancin kudi lamari ne na tsaro, wanda za a tattauna da hukumomin tsaro.

Ya ce jami’an tsaro sun bai wa hukumar tabbacin shirinsu na tabbatar da tsaro a duk fadin kasar nan.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Tsarin Sauyin Kudi Ya Taimaka Wa ‘Yan Kasa Wajen Zama Cikin Aminci – CIS Sunday,

Tsarin Sauyin Kudi Ya Taimaka Wa ‘Yan Kasa Wajen Zama Cikin Aminci - CIS Sunday,

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.