• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karbar Haraji Mai Yawa Ne Ya Durkusar Da Masana’antu A Nijeriya – Kwamiti

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Karbar Haraji Mai Yawa Ne Ya Durkusar Da Masana’antu A Nijeriya – Kwamiti
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin shugaban kasa kan inganta karbar haraji da dokokin kudi ya shawarci gwamnatin Nijeriya da ta zabtare wasu jerin haraji har 190 da ake karba daga hannun talakawan kasar nan.

Wannan dai ta zama wata hanya da za a bi wajen sakarwa masu kamfanonin da masana’antu mara, ta yadda za su samu damar gudanar da ayyukansu da kuma samun riba cikin sauki.

  • Kotun Koli Ta Tsayar Da Ranar Alhamis Don Yanke Hukunci Kan Zaben Shugaban Kasa
  • Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Fika Ya Rasu Yana Da Shekara 90

A cikin wani rahoto bayan bincike da kwamitin ya gabatar wa shugaba Tinubu, ya zargi jihohi da karbar harajin da ya wuce kima, kuma bisa rashin ka’ida.

Rahoton kwamitin ya ce wannan harajin barkatai da jihohi ke karba, shi ne sanadin tashin farashin kayayyaki da rashin samun ribar da ta dace da kuma lalacewar darajar Naira da sauran matsaloli.

Kwamitin ya yi misali da korafin da kamfanonin sadarwa suka jima suna yi game da yadda jihohi suka mayar da su saniyar tatsa ta yadda suke karbar jerin haraji.

Labarai Masu Nasaba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Yayin da yake gabatar da korafin kamfanonin sadarwar, shugaban kungiyar kamfanonin, Gbolahan Awonuga ya ce kowanne kamfanin sadarwa yana biyan haraji daban-daban har guda 40 ko sama da haka duk wata, abin da ya ce yana haddasa musu karancin abokan ciniki saboda tsada.

Shugaban kwamitin shugaban kasa Mista Taiwo Oyedele ya ce kwamitin na shawartar gwamnatin tarayya ta hade haraji fiye da 200 daban-daban da masu kamfanoni ke biya zuwa 10.

Kwamitin ya kuma bukaci gwamnatin tarayya ta yi gaggawar mayar da hankalin kan fannin tattalin arziki, don shawo kan matsalar hauhawar farashin kayayyaki da kuma lalacewar darajar Naira.

Ana ci gaba da kokawa kan yadda farashin kayan masarufi ke yin tashin gwauron zabi, lamarin da ya sanya dubban mutane gaza cin abinci sau uku a rana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HarajiKwamitiMasana'antuTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Koli Ta Tsayar Da Ranar Alhamis Don Yanke Hukunci Kan Zaben Shugaban Kasa

Next Post

Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka

Related

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Manyan Labarai

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

4 hours ago
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820
Manyan Labarai

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

6 hours ago
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki
Manyan Labarai

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

7 hours ago
Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo
Manyan Labarai

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

17 hours ago
Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC
Manyan Labarai

Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC

18 hours ago
ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
Manyan Labarai

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

24 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka

Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka

LABARAI MASU NASABA

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

July 9, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya BuÆ™aci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.