A yau Litinin, ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin ta bayyana cewa, Amurka ta yi matukar kawo cikas ga yarjejeniyar da aka cimma a tsakaninsu yayin tattaunawar tattalin arziki da cinikayya a birnin Geneva, ta hanyar gabatar da matakan nuna wariya da dama a kan kasar ta Sin.
Mai magana da yawun ma’aikatar ya bayyana cewa, wadannan matakan sun hada da fitar da wasu tsare-tsare na dakile fitar da kayayyakin fasahar sadarwa na kirkirarriyar basira, watau AI Chip, da hana sayar da zayyanar manhajar fasahar ta Chip ga kasar Sin, da kuma sanar da soke takardar biza ga daliban kasar Sin.
- Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya
- Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP — Wike
Kazalika, jami’in ya ce, wadannan abubuwan da Amurka ta aikata sun yi matukar keta yarjejeniyar da aka cimma yayin wata tattaunawa ta wayar tarho tsakanin shugabannin kasashen biyu a ranar 17 ga watan Janairu, kuma sun yi mummunan cutar da muradu da danne hakkin kasar Sin.
Ya kara da cewa, Amurka ita kadai tsiga tsiyau ta rika tayar da husuma da sabbin tashe-tashen hankula na tattalin arziki da cinikayya ba sau daya ba, ba sau biyu ba, lamarin da ya kara ta’azzara rashin tabbas da tayar da zaune tsaye ta fuskar dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin kasashen biyu.
Mai magana da yawun ma’aikatar ya kuma ce, “Maimakon ta yi wa kanta hisabi a kan abubuwan da take tafkawa, sai kuma Amurka ta zargi kasar Sin da karya yarjejeniyar, ikirarin da yake cike da yi wa gaskiya ungulu da kan zabo. Kuma tabbas, kasar Sin ta kafe kai da fata wajen yin fatali da wadannan zarge-zarge na rashin adalci.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp