ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Wike

Ministan babban birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana cewa babu wani mutum a cikin jam’iyyar PDP da zai iya korar shi ko tambayar matsayin sa a jam’iyyar. A wata ganawa da manema labarai da aka yi a Abuja, Wike ya bayyana kansa a matsayin ɗaya daga cikin mambobin da suka fi kishin PDP, yana mai cewa babu wanda ya yi wa jam’iyyar hidima fiye da abin da ya bayar.

Wike ya mayar da martani kan wani jigo na jam’iyyar, Cif Bode George, dangane da batun rashin biyan harajin ƙasa a Abuja. Ya bayyana cewa Cif Bode George na daga cikin waɗanda aka soke takardun filayensu saboda rashin biyan kuɗi na tsawon shekaru goma, yana mai cewa bai dace mutum da irin wannan matsayi ya gaza biyan hakkin ƙasa ba.

  • NLC Ta Yi Zanga-Zanga A Ofishin Wike, Ta Nemi A Biya Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi Albashin N70,000
  • Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

Ministan ya kuma soki sakamakon da PDP ke samu a jihar Legas tun daga 1999, yana mai cewa jam’iyyar bata taɓa samun nasara ba a majalisun dokoki ko tarayya ba. Ya ce wannan yana nuna cewa ba jam’iyya ce ta gina mutum ba, sai dai mutum ne ke gina jam’iyyar ta hanyar aiki da ƙoƙari.

ADVERTISEMENT

Ko da yake Wike har yanzu yana PDP, ya ce babban burinsa yanzu shi ne goyon bayan Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Ya bayyana cewa shi mutum ɗaya kawai yake biyayya masa a yanzu, wato Shugaban Ƙasa, kuma yana aiki don tallafa wa gwamnati domin kawo sauye-sauyen ci gaba.

A ƙarshe, Wike ya jaddada cewa ba za a iya fitar da shi daga PDP ba saboda irin gudummawar da ya bayar tun da farko. Ya ce yana jin daɗin faɗa da manya idan sun raina doka, yana mai cewa irin wannan halin na raina doka ne ke hana ƙasar ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

Wike
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka
  • Abubakar Sulaiman
    Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi
  • Abubakar Sulaiman
    Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma'aikatan Shari'a

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.