ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Ruwan sama

Hukumar hasashen yanayi ta ƙasa (NiMet) ta fitar da hasashen sauyin yanayi na kwanaki uku, inda ta bayyana cewa za a fuskanci ruwan sama da hadari tun daga Litinin zuwa Laraba a sassa daban-daban na Nijeriya.

A cewar NiMet, ranar Litinin za a samu hazo da ruwan sama da safe a wasu sassan jihohin Taraba, Kaduna, Gombe, Bauchi, Kebbi, Sokoto, Katsina, Jigawa da Kano a Arewa. Daga bisani a rana, za a ci gaba da samun hadari da ruwan sama a jihohin Taraba, Kaduna, Sokoto, Borno, Kebbi da Zamfara.

  • Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
  • Zafin Rana Zai Tsananta A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

A yankin Arewa ta tsakiya, jihohin Abuja, Neja da Nasarawa za su fuskanci ruwan sama da hazo da safe. Yamma kuma za a samu hadari da ruwan sama a Filato, Abuja, Nasarawa, Kwara, Neja, Kogi da Benue.

ADVERTISEMENT

A Kudu, za a fara da samun gajimare da ruwan sama a wasu sassan Ondo, Ogun, Edo, Ebonyi, Abia, Cross River, Rivers da Akwa Ibom. Daga bisani kuma, ana sa ran ruwan sama a Oyo, Ekiti, Osun, Lagos, Edo, Imo, Enugu, Delta da Bayelsa.

Ranar Talata, NiMet ta ce za a fuskanci hazo da ruwan sama da safe a jihohin Kano, Zamfara, Katsina, Bauchi, Gombe, Adamawa, Borno, Yobe da Taraba. Yamma kuma, za a samu ruwan sama a jihohin Taraba, Kebbi, Borno, Adamawa, Kaduna da Bauchi. Arewa ta tsakiya za ta ci gaba da hadari da ruwa a Abuja, Neja da Nasarawa, yayin da jihohin Kogi, Kwara da Filato za su bi sahu da rana.

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

Ranar Laraba, ruwan sama da hazo za su afkawa jihohin Zamfara, Adamawa, Kaduna, Sokoto, Kebbi da Taraba. Daga baya kuma, za a samu ruwan sama a jihohin Katsina, Bauchi da Sakkwato. Arewa ta rsakiya za ta fuskanci ruwan sama a Abuja, Nasarawa, Neja da Binuwe da safe, yayin da yamma za ta shafi Nasarawa, Filato, Kwara da Kogi.

A Kudu, ana hasashen ruwan sama da safe a Ogun, Ondo, Oyo, Edo, Enugu, Ebonyi, Cross River, Rivers da Akwa Ibom, sannan daga bisani a rana, za a sami ruwan sama a fadin yankin.

NiMet ta gargjama’a su ɗauki matakan kariya, musamman inda hadari zai faru, domin iska mai ƙarfi na iya gabatar da haɗari. An shawarci mutane su guji tuƙi a lokacin ruwan sama mai ƙarfi, su cire na’urori daga soket, su guji tsayuwa kusa da manyan itatuwa, sannan masu jirgin sama su nemi rahoton yanayi daga NiMet kafin tafiya. Ana kuma shawarci jama’a su dinga bin sahihan bayanan yanayi daga shafin NiMet:

www.nimet.gov.ng.

 

Ruwan sama
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
  • Abubakar Sulaiman
    Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Labarai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
'yansanda
Labarai

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Next Post
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.