• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Mai Fada Da Cikawa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Mai Fada Da Cikawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A karo na uku a dan tsakanin nan, wani babban jami’in Amurka na ziyara a kasar Sin. Sai dai a wannan karo, mai ziyarar shi ne jakadan Amurka mai kula da batun sauyin yanayi wato John Kerry. Ana sa ran yayin ziyararsa daga ranar 16 zuwa 19 ga wata, zai tattauna da bangaren kasar Sin kan batun sauyin yanayi, musamman game da yadda za a rage fitar da hayakin carbon a matsayinsu na kasashen da suka fi fitar da hayaki a duniya.

A ganina, ziyarar ta John Kerry ta zo a kan gaba, kuma a inda ya dace, la’akari da namijin kokarin da kasar Sin ke ci gaba da yi da zummar shawo kan matsalar.

  • Firaministan Sin Ya Gana Da Wakilin Amurka Kan Sauyin Yanayi

Wani abu da na fahimta dangane da kasar Sin shi ne, ba ta daukar alkawarin fatar baki, ita mai fada da cikawa ce. Ina sa ran kasar Sin za ta cimma burinta na kaiwa matsayin koli wajen fitar da hayakin carbon a shekarar 2030, tare da a samun daidaito tsakanin yawan hayakin da za ta fitar da abubuwan da za su shawo kansa ya zuwa 2060. Tabbas tuni kasar Sin ta dau hanya domin ta dade da fara aiwatar da abubuwa, kamar dashen bishiyoyi da dazuzukan da kyautata jituwa tsakanin dan adam da muhallinsa da sarrafa shawa da amfani da kyautata amfani da makamashi mai tsafta da sauransu. Ina da yakinin Sin za ta cimma burinta kafin lokacin da ta ayyana.

Kuma na lura cikin dukkan wasu ayyukan kasar, ta kan mayar da hankali ne wajen ganin ta rage fitar da hayakin da ma duk wani abu da ka iya gurbata muhalli. Wannan ya tuna min da ziyarata ta baya-bayan nan a birnin Chengdu na lardin Sichuan, wato birnin da zai karbi bakuncin gasar wasannin daliban jami’o’i ta duniya, inda na ga yadda kasar ta shirya tsaf domin takaita abubuwan da ka iya gurbata muhalli. Misali, yadda motocin sufurin yayin gasar ke amfani da makamashi mai tsafta da yadda aka samar da na’urorin samar da lantarki daga makamashi mai tsafta da sauransu.

Haka zalika, su ma jama’ar kasar Sin suna kokarin rungumar hanyar da ta dace na rage fitar da hayaki mai guba. Misali, bayanai sun nuna cewa, a rabin farkon bana kadai, an yi wa kimanin sabbin motoci miliyan 3.13 masu amfani da sabon makamashi rejista, adadin da ya karu da kaso 41.6 a kan na bara, wanda kuma ya kai matsayin koli.

Labarai Masu Nasaba

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

Dama dai Amurka ce ke jan kafa kan batun sauyin yanayi inda take kokarin mayar da hannu agogo baya game da yarjejeniyoyin da aka cimma da kuma kin cika alkawurranta. Fatan ita ce yadda manyan jami’anta ke zarya a kasar Sin, ya kasance ta cika alkawuranta ta kuma dauki darasi daga kasar Sin, tare da hada hannu da ita wajen tabbatar da kafuwar duniya mai aminci da tsaro makoma ta bai daya ga daukacin bil adama.

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Uba Sani Ya Rantsar Da Manyan Jami’an Gwamnati Biyu A Jihar Kaduna

Next Post

Gwamnan Zamfara Ya Kai Wa Mangal Ziyarar Ta’aziyya

Related

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

16 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

18 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

19 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

20 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

2 days ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

2 days ago
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Kai Wa Mangal Ziyarar Ta’aziyya

Gwamnan Zamfara Ya Kai Wa Mangal Ziyarar Ta'aziyya

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.