• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Mai Fada Da Cikawa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Mai Fada Da Cikawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A karo na uku a dan tsakanin nan, wani babban jami’in Amurka na ziyara a kasar Sin. Sai dai a wannan karo, mai ziyarar shi ne jakadan Amurka mai kula da batun sauyin yanayi wato John Kerry. Ana sa ran yayin ziyararsa daga ranar 16 zuwa 19 ga wata, zai tattauna da bangaren kasar Sin kan batun sauyin yanayi, musamman game da yadda za a rage fitar da hayakin carbon a matsayinsu na kasashen da suka fi fitar da hayaki a duniya.

A ganina, ziyarar ta John Kerry ta zo a kan gaba, kuma a inda ya dace, la’akari da namijin kokarin da kasar Sin ke ci gaba da yi da zummar shawo kan matsalar.

  • Firaministan Sin Ya Gana Da Wakilin Amurka Kan Sauyin Yanayi

Wani abu da na fahimta dangane da kasar Sin shi ne, ba ta daukar alkawarin fatar baki, ita mai fada da cikawa ce. Ina sa ran kasar Sin za ta cimma burinta na kaiwa matsayin koli wajen fitar da hayakin carbon a shekarar 2030, tare da a samun daidaito tsakanin yawan hayakin da za ta fitar da abubuwan da za su shawo kansa ya zuwa 2060. Tabbas tuni kasar Sin ta dau hanya domin ta dade da fara aiwatar da abubuwa, kamar dashen bishiyoyi da dazuzukan da kyautata jituwa tsakanin dan adam da muhallinsa da sarrafa shawa da amfani da kyautata amfani da makamashi mai tsafta da sauransu. Ina da yakinin Sin za ta cimma burinta kafin lokacin da ta ayyana.

Kuma na lura cikin dukkan wasu ayyukan kasar, ta kan mayar da hankali ne wajen ganin ta rage fitar da hayakin da ma duk wani abu da ka iya gurbata muhalli. Wannan ya tuna min da ziyarata ta baya-bayan nan a birnin Chengdu na lardin Sichuan, wato birnin da zai karbi bakuncin gasar wasannin daliban jami’o’i ta duniya, inda na ga yadda kasar ta shirya tsaf domin takaita abubuwan da ka iya gurbata muhalli. Misali, yadda motocin sufurin yayin gasar ke amfani da makamashi mai tsafta da yadda aka samar da na’urorin samar da lantarki daga makamashi mai tsafta da sauransu.

Haka zalika, su ma jama’ar kasar Sin suna kokarin rungumar hanyar da ta dace na rage fitar da hayaki mai guba. Misali, bayanai sun nuna cewa, a rabin farkon bana kadai, an yi wa kimanin sabbin motoci miliyan 3.13 masu amfani da sabon makamashi rejista, adadin da ya karu da kaso 41.6 a kan na bara, wanda kuma ya kai matsayin koli.

Labarai Masu Nasaba

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Dama dai Amurka ce ke jan kafa kan batun sauyin yanayi inda take kokarin mayar da hannu agogo baya game da yarjejeniyoyin da aka cimma da kuma kin cika alkawurranta. Fatan ita ce yadda manyan jami’anta ke zarya a kasar Sin, ya kasance ta cika alkawuranta ta kuma dauki darasi daga kasar Sin, tare da hada hannu da ita wajen tabbatar da kafuwar duniya mai aminci da tsaro makoma ta bai daya ga daukacin bil adama.

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Uba Sani Ya Rantsar Da Manyan Jami’an Gwamnati Biyu A Jihar Kaduna

Next Post

Gwamnan Zamfara Ya Kai Wa Mangal Ziyarar Ta’aziyya

Related

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu
Daga Birnin Sin

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

6 hours ago
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

8 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

8 hours ago
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

20 hours ago
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

21 hours ago
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

22 hours ago
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Kai Wa Mangal Ziyarar Ta’aziyya

Gwamnan Zamfara Ya Kai Wa Mangal Ziyarar Ta'aziyya

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.