• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Na Taimakawa Kasashen Afirka Bunkasa Sabon Karfin Samar Da Hajoji Da Hidimomi Masu Karko

by CGTN Hausa
2 years ago
in Ra'ayi Riga
0
Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin rahoton aikin gwamnatin kasar Sin na shekarar 2024, an ce za a yi kokarin raya tsarin masana’antu na zamani a kasar, da gaggauta raya sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko. Kana shugaban kasar Sin Xi Jinping shi ma ya jaddada bukatar aiwatar da manufar bisa yanayin da mabambantan yankuna suke ciki. 

Dangane da hakan, wani shehun malami a tarayyar Najeriya mai suna Samson Ibion ya ce, ta la’akari da matsayin kasar Sin na daya daga cikin kasashen da suka samar da mafi yawan gudunmowa ga karuwar tattalin arzikin duniya, manufar da kasar ta dauka ta raya sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, za ta amfani sauran kasashe masu tasowa. Lallai na yarda da ra’ayinsa.

  • Xi Ya Tattauna Harkokin Kasa Tare Da Wakilai Da Mambobin Manyan Taruka Biyu Na Kasar Sin
  • An Wallafa Littafi Na 1 Da Na 2 Na Littafin “Zababbun Kalamai Daga Jawaban Xi Jinping” Cikin Harshen Ingilishi

Alal misali, aikin samar da motoci masu yin amfani da makamashi mai tsabta dake tasowa cikin sauri a kasar Sin, shi ma ya samar da damammaki na samun ci gaba a kasashen Afirka.

A wajen taron makamashi na nahiyar Afirka na shekarar 2024, wanda ya gudana a birnin Cape Town na kasar Afirka ta Kudu a kwanan baya, fasahohin kera motoci masu aiki da wutar lantarki na kasar Sin da aka nuna a wajen taron sun janyo hankalin dimbin kwararru na kasashen Afirka. Aminene Merwe, ita ce darektar kamfanin Green Cab mai fasahohin kare muhalli na kasar Afirka ta Kudu. Ta ce motocin wutar lantarki na kasar Sin suna da makoma mai haske a kasuwannin kasar Afirka ta Kudu, saboda a cewarta, idan an kwatanta da motoci na sauran kasashe, “motocin kasar Sin suna da fifiko, ta fuskar yawan motocin da ake sayarwa, da farashi, da inganci, gami da karfin baturansu. ”

A lokaci guda, kamfanonin kasar Sin sun fara hadin gwiwa da takwarorinsu na kasar Habasha, don samar da motocin wutar lantarki a can. Kasancewar kasar Habasha ta samu isasshiyar wutar lantarki, ta hanyar samar da ita ta karfin ruwa, ya sa gwamnatin kasar ke sa ran ganin wata makoma mai haske game da aikin samar da motocin wutar lantarki a kasar, inda take taimakon raya bangaren ta hanyar samar da wasu manufofi na gatanci. A nasu bangare, kamfanonin kasar Sin sun samu yafuwar harajin kwastam na shigo da sassan mota da aka yi musu, ta hanyar kafa ma’aikatun hada sassan motoci a kasar Habasha. Lamarin da ya ba su damar rage kudin da ake kashewa wajen samar da motoci, da farashin motocin da ake samarwa, gami da raya masana’antu, da samar da karin guraben aikin yi a kasar.

Labarai Masu Nasaba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Ta wadannan misalai za mu iya ganin cewa, da farko, yayin da kasar Sin ke kokarin neman raya sabon karfin samar da hajoji, da hidimomi masu karko, ita ma ta kai shi kasashen Afirka. Na biyu shi ne, ingancin kayayyakin Sin, da farashinsu, da fasahohin kasar, da tsarinta na zuba jari, dukkansu sun dace da ainihin yanayin da ake ciki a kasashen Afirka. Wannan ya kasance dabarar da ake dauka ta raya harkoki bisa yanayi da muhalli da ake ciki.

Bari mu dauki wani batu da ya shafi aikin sadarwa a matsayin misali. Kamfanin tantance yanayin kasuwannin kimiyya da fasaha na kasa da kasa Canalys, ya gabatar da wasu alkaluma a kwanan baya, wadanda suka nuna cewa, kamfanin samar da wayoyin salula na Transsion na kasar Sin, ya sayar da wayoyin salula har miliyan 34 da dubu 500 a kasashen Afirka a shekarar 2023, adadin da ya kai rabin wayoyin da aka sayar da su a nahiyar. Ta haka, kamfanin ya zama wanda ya sayar da mafi yawan wayoyin salula a nahiyar Afirka.

To, ko me ya sa wayoyin salula na kamfanin ke samun karbuwa a kasuwannin Afirka? Dalilin shi ne yadda kamfanin ke mai da cikakken hankali kan bukatu na mutanen nahiyar Afirka. Wayoyin salula na kamfanin, suna da fifiko, wato da farko ya fi biyan bukatun al’umma bakaken fata wajen daukar hotuna. Na biyu, ana iya sanya katuna na SIM da yawa a cikin wayar salula guda. Na uku, wayoyin salular suna kunshe da tsarin sarrafawa na harsunan Afirka. Yayin da na hudu, suke da batura masu karfi da dorewa. Na biyar, a cikin wayoyin salular akwai APP mai kunshe da dimbin wakokin kasashen Afirka. Na shida shi ne, akwai wayoyin salula iri-iri da za a iya zaba, kana dukkansu na da inganci da araha. To, duk wadannan halaye ne na musamman da suka dace da bukatun mutanen kasashen Afirka, da muhallin wuraren zaman su, wadanda suka sa wayoyin salula kirar kamfanin ke samun karbuwa a kasashen Afirka.

A sa’i daya kuma, wannan kamfani na kasar Sin ya kafa cibiyoyin kirkire-kirkire, da masana’antu, da sassa masu kula da sayarwa, da samar da hidimomi, a kasashen Najeriya, da Kenya, da Habasha, da dai sauransu, ta yadda aka kai fasahar sadarwa ta zamani a nahiyar Afirka, da samar da guraben aikin yi da damammaki na raya kai ga matasan nahiyar.

To, duk wadannan misalai ne na yadda kasar Sin take kokarin raya masana’antun zamani da sabon karfin samar da hajoji, da hidimomi masu karko a kasashen Afirka, bisa yanayin da kasashen suke ciki.

Wani shehun malami mai suna Robert Gituru, wanda ke jami’ar fasahohin aikin noma ta Jomo Kenyatta ta kasar Kenya, yayin da yake hira da manema labaru a kwanakin baya, ya ce, bisa matsayinta na kasa dake kan hanyar tasowa, kasar Sin ta fi sauran sassa fahimtar kalubalolin da kasashen Afirka suke fuskanta, kana tana da dabarun warware matsaloli da za su biya bukatun kasashen Afirka.

A ganina, wannan shi ne dalilin da ya sa fasahohin kasar Sin, da manufofinta ke samun karbuwa, gami da samar da hakikanin gudunmowa a kasashen Afirka. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Kula Da Wutar Lantarki Ta Kaduna Ta Yi Allah-wadai Da Yajin aikin Ma’aikata

Next Post

Sheikh Gumi Ga Tinubu: Ka Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga, Kada Ka Zama Irin Buhari

Related

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

3 days ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

7 days ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

7 days ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

1 week ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

1 week ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

1 week ago
Next Post
Sheikh Gumi Ga Tinubu: Ka Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga, Kada Ka Zama Irin Buhari

Sheikh Gumi Ga Tinubu: Ka Yi Sulhu Da 'Yan Bindiga, Kada Ka Zama Irin Buhari

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

September 12, 2025
Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.