• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Afirka Na Cin Gajiyar Aikin Zamanintar Da Aikin Gona Na Sin

by CGTN Hausa
2 years ago
Gona

Innocent Mojidi dan kasar Najeriya ne mai shekaru 35 da haifuwa, ya taba zuwa kasar Sin sau biyu don samun horo a fannin aikin gona, yauzu yana noman shimkafa da masara a gonakinsa dake karkarar birnin Abuja hedkwatar Najeriya. Saboda kwarewar da ya samu, ya zama masanin aikin gona a garinsu. ‘Yan Afrika da dama ne kamar Innocent Mojidi suka zo kasar Sin don koyon dabarun aikin noma na zamani, matakin da ya taimaka musu wajen tinkarar matsalar karancin isasshen hatsi.

A cikin shekaru 10 da suka gabata bayan Sin da Afrika suka yi hadin gwiwa a fannin aikin noma, Sin ta kulla yarjeniyoyi 34 da kasashen Afrika da AU da AGRA a wannan bangare, da kuma yin mu’ammala kan samar da isasshen hatsi da rage talauci da tinkarar sauyin yanayi da sauransu. Ban da wannan kuma, ma’aikatar aikin noma da raya kauyuka ta kasar sin ta tura masananta fiye da 400 zuwa kasashen Afrika tare da horar da ‘yan Afrika fiye da dubu 10.

  • Yanzu-yanzu: Kotun Daukaka Kara Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Zaben Gwamnan Kano Gobe A Abuja
  • Xi Jinping Ya Fara Ganawa Da Joe Biden

Ban da samar da dabaru na kimiyya da fasaha, Sin ta taimakawa kasashen Afrika wajen gina wasu manyan ababen more rayuwa a wannan fanni. Gwamnatin Sin ta tallafawa Najeriya wajen gina cibiyar raya aikin gona ta gwaji a Abuja kyauta, wannan cibiyar ta fitar da wani nau’in irin shimkafa samfurin Gawal R1, kuma an yi shekaru 5 ana shuka wannan iri a Najeriya, wanda ya samar da karin shinkafa tan miliyan 2, inda manoma fiye da dubu 200 suka ci gajiya. A cikin shekaru 10 da suka gabata, Sin ta taimakawa kasashen Afrika wajen gina cibiyoyin gwaji a fannin aikin noma 24, inda aka gabatar tare da yayata fasahohi fiye da 300 a wuraren, yawan karuwar hatsi da aka samu ya kai kashi 30% zuwa 60%, manoma kimanin miliyan 1 sun ci gajiyar wadannan fasahohi.

Yanzu, gwamnatin Sin na kara karfafa hadin gwiwa da kasashen Afrika a wannan fanni, kuma ta gudanar da dandalin hadin kan Sin da Afrika a fannin aikin gona karo na 2 a birnin Sanya na lardin Hainan dake kudancin kasar Sin daga ran 13 zuwa 15. Dandalin na da zummar habaka hadin kan bangarorin biyu, ta yadda za a kara inganta ayyukan gona a kasashen Afrika, tare da cimma muradun samun ci gaba nan da shekara ta 2030 a wannan bangare a kasashen Afrika.

Ayyukan hadin kai a bangaren aikin noma karkashin shirin hadin kan kasashe masu tasowa da shawarar “ziri daya da hanya daya” sun samarwa kasashe masu tasowa musamman ma kasashen Afrika tallafin manyan ababen more rayuwa a fannin aikin noma da kudade da fasahohi da hatsi da sauransu, matakan da za su taimaka musu wajen samun bunkasuwa da dogara da karfin kansu. Labarin Mojidi da cibiyar gwaji ta fasahohin aikin noma dake Abuja sun zama misali ta fuskar hadin kan Sin da Afrika. Ana sa ran cewa, a cikin shekaru 10 masu zuwa, bangarorin biyu za su samu karin ci gaba a wannan fanni. (Mai zana da rubuta: MINA)

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani
Daga Birnin Sin

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Next Post
Sin Da Afirka Na Da Makoma Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwar Aikin Gona

Sin Da Afirka Na Da Makoma Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwar Aikin Gona

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Gona

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.