• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Afirka Na Cin Gajiyar Aikin Zamanintar Da Aikin Gona Na Sin

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasashen Afirka Na Cin Gajiyar Aikin Zamanintar Da Aikin Gona Na Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Innocent Mojidi dan kasar Najeriya ne mai shekaru 35 da haifuwa, ya taba zuwa kasar Sin sau biyu don samun horo a fannin aikin gona, yauzu yana noman shimkafa da masara a gonakinsa dake karkarar birnin Abuja hedkwatar Najeriya. Saboda kwarewar da ya samu, ya zama masanin aikin gona a garinsu. ‘Yan Afrika da dama ne kamar Innocent Mojidi suka zo kasar Sin don koyon dabarun aikin noma na zamani, matakin da ya taimaka musu wajen tinkarar matsalar karancin isasshen hatsi.

A cikin shekaru 10 da suka gabata bayan Sin da Afrika suka yi hadin gwiwa a fannin aikin noma, Sin ta kulla yarjeniyoyi 34 da kasashen Afrika da AU da AGRA a wannan bangare, da kuma yin mu’ammala kan samar da isasshen hatsi da rage talauci da tinkarar sauyin yanayi da sauransu. Ban da wannan kuma, ma’aikatar aikin noma da raya kauyuka ta kasar sin ta tura masananta fiye da 400 zuwa kasashen Afrika tare da horar da ‘yan Afrika fiye da dubu 10.

  • Yanzu-yanzu: Kotun Daukaka Kara Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Zaben Gwamnan Kano Gobe A Abuja
  • Xi Jinping Ya Fara Ganawa Da Joe Biden

Ban da samar da dabaru na kimiyya da fasaha, Sin ta taimakawa kasashen Afrika wajen gina wasu manyan ababen more rayuwa a wannan fanni. Gwamnatin Sin ta tallafawa Najeriya wajen gina cibiyar raya aikin gona ta gwaji a Abuja kyauta, wannan cibiyar ta fitar da wani nau’in irin shimkafa samfurin Gawal R1, kuma an yi shekaru 5 ana shuka wannan iri a Najeriya, wanda ya samar da karin shinkafa tan miliyan 2, inda manoma fiye da dubu 200 suka ci gajiya. A cikin shekaru 10 da suka gabata, Sin ta taimakawa kasashen Afrika wajen gina cibiyoyin gwaji a fannin aikin noma 24, inda aka gabatar tare da yayata fasahohi fiye da 300 a wuraren, yawan karuwar hatsi da aka samu ya kai kashi 30% zuwa 60%, manoma kimanin miliyan 1 sun ci gajiyar wadannan fasahohi.

Yanzu, gwamnatin Sin na kara karfafa hadin gwiwa da kasashen Afrika a wannan fanni, kuma ta gudanar da dandalin hadin kan Sin da Afrika a fannin aikin gona karo na 2 a birnin Sanya na lardin Hainan dake kudancin kasar Sin daga ran 13 zuwa 15. Dandalin na da zummar habaka hadin kan bangarorin biyu, ta yadda za a kara inganta ayyukan gona a kasashen Afrika, tare da cimma muradun samun ci gaba nan da shekara ta 2030 a wannan bangare a kasashen Afrika.

Ayyukan hadin kai a bangaren aikin noma karkashin shirin hadin kan kasashe masu tasowa da shawarar “ziri daya da hanya daya” sun samarwa kasashe masu tasowa musamman ma kasashen Afrika tallafin manyan ababen more rayuwa a fannin aikin noma da kudade da fasahohi da hatsi da sauransu, matakan da za su taimaka musu wajen samun bunkasuwa da dogara da karfin kansu. Labarin Mojidi da cibiyar gwaji ta fasahohin aikin noma dake Abuja sun zama misali ta fuskar hadin kan Sin da Afrika. Ana sa ran cewa, a cikin shekaru 10 masu zuwa, bangarorin biyu za su samu karin ci gaba a wannan fanni. (Mai zana da rubuta: MINA)

Labarai Masu Nasaba

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Wang yiXi JinpingXinhua
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

Next Post

Sin Da Afirka Na Da Makoma Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwar Aikin Gona

Related

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

4 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

5 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

6 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

7 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

8 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

9 hours ago
Next Post
Sin Da Afirka Na Da Makoma Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwar Aikin Gona

Sin Da Afirka Na Da Makoma Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwar Aikin Gona

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.