• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Afrika Sun Ce Wa Kasar Amurka “Babu ruwanki”

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasashen Afrika Sun Ce Wa Kasar Amurka “Babu ruwanki”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokai na, kun fahimci damuwar iyayen yara kuwa? Wato yadda suke damuwa kan wasu abubuwan da yaransu ke yi, kamar son wasa maimakon yin karatu, da yawan mu’amala da wayar salula, da dai sauransu, abin da kan sa su zagin yara. Wannan damuwa ce da za a iya fahimta. Sai dai abin mamaki shi ne, wasu kasashe ma su kan nuna wannan nau’in damuwa na iyaye. Wato su kan kalli kansu tamkar “iyayen” sauran kasashe, inda suke son tsoma baki a harkokin cikin gida na sauran kasashen. 

Misali, lokacin da Kamala Harris, mataimakiyar shugaban kasar Amurka, take ziyara a kasar Ghana a kwanakin baya, ta matsawa bangaren Ghana lamba kan batun kare hakkin ‘yan luwadi. Dalilin da ya sa haka, shi ne domin majalisar dokokin kasar Ghana na tattaunawa kan daftarin dokar haramta masu neman jinsi daya. Dangane da wannan batu, Harris ta nuna goyon baya ga‘yan luwadi, inda ta ce, “ A ganin kasar Amurka, batun kare hakkin‘yan luwadi, wani batu ne da ya shafi hakkin dan Adam, don haka kasarmu ba za ta taba ja da baya ba.”

  • Afirka Ta Kudu Na Maraba Da Zuwan Sinawa Masu Yawon Shakatawa Kasar

Mun san kasar Amurka ta saba da yin katsalandan cikin harkokin gida na sauran kasashe, har ma da daukar matakan soja kan sauran kasashe, ta hanyar fakewa da kalmar “kare hakkin dan Adam”. Saboda haka kasar ba ta ganin wani kuskure a maganar Madam Harris. Sai dai kalaman nata ya fusata ‘yan kasar Ghana, inda Alban Bagbin, shugaban majalisar dokokin kasar Ghana, ya ce ba zaitaba yarda da maganar Madam Harris ba. A cewarsa, kasar Amurka na neman baiwa kasar Ghana umarni ne, lamarin da ya sabawa ruhi na Demokuradiyya.

Sa’an nan wani batu na daban da ya sa kasar Amurka damuwa shi ne huldar dake tsakanin kasashen Afrika da kasar ta Sin. Ko da yake, Kamala Harris ta ce ziyararta a nahiyar Afrika ba ta shafi kasar Sin ba. Amma rahotannin da kafofin watsa labaru na kasar Amurka suka gabatar sun nuna wata damuwa mai tsanani kan tasirin kasar Sin a kasashen Afirka. Inda kamfanin dillancin labaru na AP ya ce, lokacin da Madam Harris ke ziyara a kasar Zambia, jirgin samanta ya sauka a wani filin jirgin sama da wani kamfanin kasar Sin ya yi masa kwaskwarima, bisa rancen kudin da kasar Sin ta bayar. A nata bangare, jaridar The New York Times, ta ce ayarin motocin Harris ya wuce wata babbar mararrabar hanya dake tsakiyar birnin Accra na kasar Ghana, inda aka rubuta a wani kwali cewa, kasar Sin ce ta ba da tallafin kudin gina mararrabar hanyar. A cewar kamfanin AP, huldar kut-da-kut dake tsakanin Afrika da Sin ta sa gwamnatin kasar Amurka damuwa sosai, saboda tana tsoron ganin yadda kasashen Afirka suka kara karkata ga bangaren kasar Sin.

Wannan damuwa mai tsanani da kasar Amurka ta nuna ya ja hankali shugaba Nana Akufo-Addo na kasar Ghana, don haka ya mayar da martani. Yayin wani taron manema labaru, kuma a gaban Madam Kamala Harris, shugaban na kasar Ghana ya ce, “ Watakila kasar Amurka za ta damu game da tasirin kasar Sin a nahiyar Afrika, amma mu ba ma damuwa. Kasar Sin tana cikin dimbin kasashen da kasar Ghana ke hulda da su, ma iya cewa dukkan kasashen duniya abokanmu ne.” Ma’ana “Akwai dimbin kasashe a duniyarmu, kuma za mu iya hulda da duk wanda muke son hulda. Wannan batu ba ruwan kasar Amurka a ciki. ”

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Bayan haka, Yemi Osinbajo, mataimakin shugaban kasar Najeriya, shi ma ya wallafa wani bayani a shafinsa na sada zumunta na Twitter, inda ya ce, “Galibin kasashen Afrika ba za su nemi a yi musu afuwa bisa huldar kut-da-kut dake tsakaninsu da kasar Sin ba. Saboda kasar Sin ta gabatar da kanta a wurare da lokutan da su kasashen yamma ba su son kasancewa ciki. Kasashen Afrika na bukatar rancen kudi, da kayayyakin more rayuwa, sa’an nan kasar Sin ta biya musu bukatunsu.”

Gaskiya kasar Amurka ta sha nuna damuwa, inda ta damu da yiwuwar abkuwar“keta hakkin dan Adam” a kasashen Afrika, da yadda suke hulda da kasar Sin, da sauran batutuwa daban daban. Sai dai kasashen Afrika sun riga sun bayyana mata cewa, “Babu ruwanki ko kadan!”Wai mai Daki shi ya san inda yake masa Yoyo. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Bayar Da Belin Mawaki Portable

Next Post

Burundi Na Yabawa Tallafin Kasar Sin A Fannin Raya Noma

Related

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

18 hours ago
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
Daga Birnin Sin

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

19 hours ago
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
Daga Birnin Sin

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

20 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

21 hours ago
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
Daga Birnin Sin

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

22 hours ago
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
Daga Birnin Sin

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

24 hours ago
Next Post
Burundi Na Yabawa Tallafin Kasar Sin A Fannin Raya Noma

Burundi Na Yabawa Tallafin Kasar Sin A Fannin Raya Noma

LABARAI MASU NASABA

An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.