ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Da Ke Kwashe Likitocin Nijeriya Za Su Fara Biyan Diyya – Ministan Lafiya

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Minista

Nijeriya ta samar da wani kudiri da aka amince da shi a makon da ya gabata wanda ya yi kira ga kasashen da suke dauke mata likitoci su rika biyan diyyar kudaden da gwamnati ta kashe wajen ilmantar da su.

Ministan Lafiya, Dakta Muhammed Ali Pate, ya bayyana haka a shirin BBC Hausa na tattaunawa a tsakanin shugabanni da al’umma kan matsalolin da ke addabar ‘yan kasa mai taken “A Fada A Cika” da aka gudanar ranar Laraba a Abuja, wanda aka gayyaci LEADERSHIP Hausa.

  • Kano: Kotun Daukaka Kara Ta Bukace Lauyoyin Su Mayar Da Kwafin Takardun Shari’ar
  • Gwamna Nasir Ya Gabatar Da Kasafin Kudin Naira Biliyan 250 Ga Majalisar Dokokin Kebbi

Yayin da aka tambaye shi wace hanya za a bi domin magance tserewar da likitoci ke yawan yi daga kasar nan zuwa wasu kasashen waje, ministan ya ce akwai matsaloli da dama da suke addabar fannin lafiya da ya kamata su likitocin su yi masu duba na tsanaki tare da nuna kishin ƙasa.

ADVERTISEMENT

“Abin da ya dace su likitocin su fara dubawa shi ne, na farko dai ko da mutum ba a makarantar gwamnati ya yi karatu ba to babu makawa gwamnati ta taka rawa a al’amarin da ya shafi iliminsa ta wata fuskar, don haka kamata ya yi su fara duba kishin kasar kafin su yi tunanin barin kasar saboda rashin albashi. Nijeriya kasarmu ce kuma babu wanda zai zo ya gyara mana in ba mu ba.

“Na biyu kuma, su tuna cewa akwa jami’an da suka sadaukar da rayuwarsu domin kare rayukan ‘yan Nijeriya kuma ake biyan su kudin da bai kai nasu yawa ba, misalin sojoji da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro, kuma aikinsu ya fi na likitocin wahala, ka ga wannan ba wani abu ne ba illa kishin kasa, domin albashin nasu ba wani yawa ne da shi ba, wannan kishin kasa ne. Don haka ya kamata kasashen da suke dauke mana likitoci su fara biyan mu kudaden da muka kashe wajen ba su ilimi domin mu samu sukunin maye gurbin wadancan da suka dauke mana. Mun cimma matsaya kan haka a makon da ya gabata kuma za mu gabatar musu da bukatar hakan,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Minista
Haruna Kakangi na BBC Hausa tare da ministan lokacin gabatar da shirin a Otel ɗin 3 Js da ke Utako Abuja

Ya ce cututtuka sun karu kuma kudaden da gwamnati ke kashewa wajen kula da lafiyar jama’a ma sun karu duk da ba su kai yadda ake so ba, “kana saboda kashi 80 cikin 100 na kayan da ake harhada magunguna shigo da su ake daga waje, ya sa magungunan sun yi tsada kuma yanzu kowa ya san yadda farashin Dala yake, don haka dole sai gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi da kuma jama’a sun taimaka wa gwamnatin tarayya.

“A kokarin da muke yi na inganta aikace-aikacen kula da lafiya, a tsakanin wata uku da rantsar da mu a matsayin ministroci, mun yi bincike kan wasu mutum 2,500 domin ganin yadda za mu raga yawan matsalolin da ake fuskanta na kiwon lafiya. Sakamakon binciken, yanzu haka mun sha damarar ganin an samar da asibito na sha-ka-tafi a kowace mazaba da ke fadin kasar nan. Wannan zai kara inganta kiwon lafiya a matakin farko.

“Kuma abin da ya kamata mutane su sani shi ne, gwamnatin tarayya ita kadai ke ba da kaso 70 na kudaden gudanar da cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko. Duk da haka wannan bai isa, a kullum Dala 10 ake kashewa ga lafiyar kowane dan Nijeriya, wannan ya yi karanci kwarai da gaske, domin Ingila Fam 5,000 take kashewa, Amurka Dala 14,000. To amma duk wannan ba za mu iya hada kanmu da sub a saboda yanayin tattalin arzikinmu, sai dai duk da haka za mu kara kokari kuma su ma jihohi su kara yawan abin da suke bayarwa ga kiwon lafiya,” in ji shi.

Da yake bayani a kan inshorar lafiya kuwa, Dakta Pate ya bayyana cewa, tun a 1974 Nijeriya ta fara shirin Inshorar lafiya. Bincike ya nuna kaso 10 ne daga cikin ‘yan Nijeriya suke da Inshorar lafiya, don haka a yanzu shugaban kasa ya rattaba hannu a kan tilas a shigar da kowane dan Nijeriya cikin Inshorar lafiya. Sannan akwai gidauniya ta tallafa wa marasa lafiya da ba su da galihu wanda a yanzu haka akwai mutum miliyan 1.7 da suke cin gajiya. Ka ga wannan bai wadatar ba”

Har ila yau, ministan ya shawarci ‘Yan Nijeriya su rika zuwa asibitoci ana duba lafiyarsu domin idan aka gano cututtuka irin su na Koda, Siga, AIDS da hawan jini, da sauransu da wuri, ana iya fara magani tun kafin abin ya ta’azzara.

Ministan ya kuma bayyana kokarin da suke yi na sarrafa magunguna a cikin gida maimakon kasashen waje, inda ya nunar da cewa akwai kusan kamfanoni 150 da za a zauna da su domin cimma wannan kudiri.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane
Labarai

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle
Labarai

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Next Post
Samar Da Ci Gaba A Bangaren Ma’adinai: Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Da Koƙarin Takwaransa Na Ma’adinai

Samar Da Ci Gaba A Bangaren Ma'adinai: Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Da Koƙarin Takwaransa Na Ma'adinai

LABARAI MASU NASABA

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

November 13, 2025
Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

November 13, 2025
Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

November 13, 2025
Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

November 13, 2025
‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.