• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Da Ke Kwashe Likitocin Nijeriya Za Su Fara Biyan Diyya – Ministan Lafiya

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Kasashen Da Ke Kwashe Likitocin Nijeriya Za Su Fara Biyan Diyya – Ministan Lafiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya ta samar da wani kudiri da aka amince da shi a makon da ya gabata wanda ya yi kira ga kasashen da suke dauke mata likitoci su rika biyan diyyar kudaden da gwamnati ta kashe wajen ilmantar da su.

Ministan Lafiya, Dakta Muhammed Ali Pate, ya bayyana haka a shirin BBC Hausa na tattaunawa a tsakanin shugabanni da al’umma kan matsalolin da ke addabar ‘yan kasa mai taken “A Fada A Cika” da aka gudanar ranar Laraba a Abuja, wanda aka gayyaci LEADERSHIP Hausa.

  • Kano: Kotun Daukaka Kara Ta Bukace Lauyoyin Su Mayar Da Kwafin Takardun Shari’ar
  • Gwamna Nasir Ya Gabatar Da Kasafin Kudin Naira Biliyan 250 Ga Majalisar Dokokin Kebbi

Yayin da aka tambaye shi wace hanya za a bi domin magance tserewar da likitoci ke yawan yi daga kasar nan zuwa wasu kasashen waje, ministan ya ce akwai matsaloli da dama da suke addabar fannin lafiya da ya kamata su likitocin su yi masu duba na tsanaki tare da nuna kishin ƙasa.

“Abin da ya dace su likitocin su fara dubawa shi ne, na farko dai ko da mutum ba a makarantar gwamnati ya yi karatu ba to babu makawa gwamnati ta taka rawa a al’amarin da ya shafi iliminsa ta wata fuskar, don haka kamata ya yi su fara duba kishin kasar kafin su yi tunanin barin kasar saboda rashin albashi. Nijeriya kasarmu ce kuma babu wanda zai zo ya gyara mana in ba mu ba.

“Na biyu kuma, su tuna cewa akwa jami’an da suka sadaukar da rayuwarsu domin kare rayukan ‘yan Nijeriya kuma ake biyan su kudin da bai kai nasu yawa ba, misalin sojoji da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro, kuma aikinsu ya fi na likitocin wahala, ka ga wannan ba wani abu ne ba illa kishin kasa, domin albashin nasu ba wani yawa ne da shi ba, wannan kishin kasa ne. Don haka ya kamata kasashen da suke dauke mana likitoci su fara biyan mu kudaden da muka kashe wajen ba su ilimi domin mu samu sukunin maye gurbin wadancan da suka dauke mana. Mun cimma matsaya kan haka a makon da ya gabata kuma za mu gabatar musu da bukatar hakan,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Minista
Haruna Kakangi na BBC Hausa tare da ministan lokacin gabatar da shirin a Otel ɗin 3 Js da ke Utako Abuja

Ya ce cututtuka sun karu kuma kudaden da gwamnati ke kashewa wajen kula da lafiyar jama’a ma sun karu duk da ba su kai yadda ake so ba, “kana saboda kashi 80 cikin 100 na kayan da ake harhada magunguna shigo da su ake daga waje, ya sa magungunan sun yi tsada kuma yanzu kowa ya san yadda farashin Dala yake, don haka dole sai gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi da kuma jama’a sun taimaka wa gwamnatin tarayya.

“A kokarin da muke yi na inganta aikace-aikacen kula da lafiya, a tsakanin wata uku da rantsar da mu a matsayin ministroci, mun yi bincike kan wasu mutum 2,500 domin ganin yadda za mu raga yawan matsalolin da ake fuskanta na kiwon lafiya. Sakamakon binciken, yanzu haka mun sha damarar ganin an samar da asibito na sha-ka-tafi a kowace mazaba da ke fadin kasar nan. Wannan zai kara inganta kiwon lafiya a matakin farko.

“Kuma abin da ya kamata mutane su sani shi ne, gwamnatin tarayya ita kadai ke ba da kaso 70 na kudaden gudanar da cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko. Duk da haka wannan bai isa, a kullum Dala 10 ake kashewa ga lafiyar kowane dan Nijeriya, wannan ya yi karanci kwarai da gaske, domin Ingila Fam 5,000 take kashewa, Amurka Dala 14,000. To amma duk wannan ba za mu iya hada kanmu da sub a saboda yanayin tattalin arzikinmu, sai dai duk da haka za mu kara kokari kuma su ma jihohi su kara yawan abin da suke bayarwa ga kiwon lafiya,” in ji shi.

Da yake bayani a kan inshorar lafiya kuwa, Dakta Pate ya bayyana cewa, tun a 1974 Nijeriya ta fara shirin Inshorar lafiya. Bincike ya nuna kaso 10 ne daga cikin ‘yan Nijeriya suke da Inshorar lafiya, don haka a yanzu shugaban kasa ya rattaba hannu a kan tilas a shigar da kowane dan Nijeriya cikin Inshorar lafiya. Sannan akwai gidauniya ta tallafa wa marasa lafiya da ba su da galihu wanda a yanzu haka akwai mutum miliyan 1.7 da suke cin gajiya. Ka ga wannan bai wadatar ba”

Har ila yau, ministan ya shawarci ‘Yan Nijeriya su rika zuwa asibitoci ana duba lafiyarsu domin idan aka gano cututtuka irin su na Koda, Siga, AIDS da hawan jini, da sauransu da wuri, ana iya fara magani tun kafin abin ya ta’azzara.

Ministan ya kuma bayyana kokarin da suke yi na sarrafa magunguna a cikin gida maimakon kasashen waje, inda ya nunar da cewa akwai kusan kamfanoni 150 da za a zauna da su domin cimma wannan kudiri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara, Gwamna Uba Sani Ya Nemi Haɗa Hannu Da ‘Yan Adawa

Next Post

Samar Da Ci Gaba A Bangaren Ma’adinai: Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Da Koƙarin Takwaransa Na Ma’adinai

Related

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya
Labarai

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

10 hours ago
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

12 hours ago
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista
Labarai

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

14 hours ago
Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi

16 hours ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

18 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

18 hours ago
Next Post
Samar Da Ci Gaba A Bangaren Ma’adinai: Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Da Koƙarin Takwaransa Na Ma’adinai

Samar Da Ci Gaba A Bangaren Ma'adinai: Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Da Koƙarin Takwaransa Na Ma'adinai

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.