• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashi 50 Na Magungunan Afrika Jabu Ne – Majalisar Dinkin Duniya

by Sadiq
3 years ago
Kashi 50

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewar sama da kashi 50 na magungunan da ake sayarwa a kasashen Afirka ta Yamma marasa inganci ne, abin da ya sa sukan bijire wa cututtuka da kuma sanya mutane rashin amincewa da tsarin kula da lafiyar da ake amfani da su.

Ofishin majalisar da ke kula da magunguna, ya ce tsakanin watan Janairun shekarar 2017 zuwa Disambar shekarar 2021 akalla tan 605 na irin wadannan magunguna marasa inganci aka kwace a yankin daga masu safarar su.

  • Jirgin Sama Kirar Kasar Sin Samfurin C919 Ya Tashi A Karon Farko Cikin Sabuwar Shekarar Zomo
  • Masani: Sin Za Ta Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Duniya A Shekarar 2023

Majalisar ta ce a kowace shekara ana kashe kudin da ya kai kusan Dala miliyan 45 wajen kula da lafiyar jama’ar da suka yi amfani da irin wadannan magunguna marasa inganci a matsayin maganin cutar zazzabin cizon sauro, yayin da ake samun mutane dubu 267 da ke mutuwa kowace shekara saboda kwankwadar magungunan.

Bayan magungunan marasa inganci, majalisar ta yi kuma gargadi a kan yadda ake amfani da wasu magunguna ta hanyoyin da ba su kamata ba, abin da ke haifar da bijirewar wadanda ake amfani da su wajen kare kai daga cutar zazzabi.

Francois Patuel, shugaban sashen bincike da kula da magungunan Majalisar, ya ce ba a iya sanya ido wajen ganin yadda ake amfani da magungunan da zarar sun bar kamfanonin da aka sarrafa su.

LABARAI MASU NASABA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

Rahotan wanda ya mayar da hankali a kan safarar magungunan ta barauniyar hanya ta kasashen Mauritania da Mali da Burkina Faso da Nijar da kuma Chadi, ya ce ana karkata su ne daga Turai da China da kuma Indiya, yayin da suke bi ta gabar ruwan kasashe irin su Guinea da Ghana da Togo da Benin da kuma Nijeriya zuwa yankin Sahel baki daya.

Majalisar ta ce mutanen da suke amfana da safarar wadannan gurbatattun magunguna sun hada da ma’aikatan kamfanonin da ake sarrafa su da jami’an tsaro da kuma masu sayar da su a kan tituna.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10
Manyan Labarai

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Next Post
An Hallaka Matashi 1, An Jikkata Wani A Yakin Zaben APC A Bauchi

An Hallaka Matashi 1, An Jikkata Wani A Yakin Zaben APC A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Yadda Ake Miyar Margi

Yadda Ake Miyar Margi

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

November 8, 2025
Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Maganin Nankarwa (4)

Maganin Nankarwa (4)

November 8, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

November 8, 2025
NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu

November 8, 2025
Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.