• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashi 50 Na Magungunan Afrika Jabu Ne – Majalisar Dinkin Duniya

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kashi 50 Na Magungunan Afrika Jabu Ne – Majalisar Dinkin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewar sama da kashi 50 na magungunan da ake sayarwa a kasashen Afirka ta Yamma marasa inganci ne, abin da ya sa sukan bijire wa cututtuka da kuma sanya mutane rashin amincewa da tsarin kula da lafiyar da ake amfani da su.

Ofishin majalisar da ke kula da magunguna, ya ce tsakanin watan Janairun shekarar 2017 zuwa Disambar shekarar 2021 akalla tan 605 na irin wadannan magunguna marasa inganci aka kwace a yankin daga masu safarar su.

  • Jirgin Sama Kirar Kasar Sin Samfurin C919 Ya Tashi A Karon Farko Cikin Sabuwar Shekarar Zomo
  • Masani: Sin Za Ta Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Duniya A Shekarar 2023

Majalisar ta ce a kowace shekara ana kashe kudin da ya kai kusan Dala miliyan 45 wajen kula da lafiyar jama’ar da suka yi amfani da irin wadannan magunguna marasa inganci a matsayin maganin cutar zazzabin cizon sauro, yayin da ake samun mutane dubu 267 da ke mutuwa kowace shekara saboda kwankwadar magungunan.

Bayan magungunan marasa inganci, majalisar ta yi kuma gargadi a kan yadda ake amfani da wasu magunguna ta hanyoyin da ba su kamata ba, abin da ke haifar da bijirewar wadanda ake amfani da su wajen kare kai daga cutar zazzabi.

Francois Patuel, shugaban sashen bincike da kula da magungunan Majalisar, ya ce ba a iya sanya ido wajen ganin yadda ake amfani da magungunan da zarar sun bar kamfanonin da aka sarrafa su.

Labarai Masu Nasaba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Rahotan wanda ya mayar da hankali a kan safarar magungunan ta barauniyar hanya ta kasashen Mauritania da Mali da Burkina Faso da Nijar da kuma Chadi, ya ce ana karkata su ne daga Turai da China da kuma Indiya, yayin da suke bi ta gabar ruwan kasashe irin su Guinea da Ghana da Togo da Benin da kuma Nijeriya zuwa yankin Sahel baki daya.

Majalisar ta ce mutanen da suke amfana da safarar wadannan gurbatattun magunguna sun hada da ma’aikatan kamfanonin da ake sarrafa su da jami’an tsaro da kuma masu sayar da su a kan tituna.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfrikaJabuMagungunaSafarar Miyagun Kwayoyi
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Sace Kananan Yara 2 A Kano

Next Post

An Hallaka Matashi 1, An Jikkata Wani A Yakin Zaben APC A Bauchi

Related

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Manyan Labarai

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

4 hours ago
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820
Manyan Labarai

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

6 hours ago
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki
Manyan Labarai

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

7 hours ago
Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo
Manyan Labarai

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

17 hours ago
Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC
Manyan Labarai

Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC

18 hours ago
ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
Manyan Labarai

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

24 hours ago
Next Post
An Hallaka Matashi 1, An Jikkata Wani A Yakin Zaben APC A Bauchi

An Hallaka Matashi 1, An Jikkata Wani A Yakin Zaben APC A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.