• Leadership Hausa
Tuesday, May 30, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Dalibai Na Da Wakilai A Tattaunawa Tsakanin ASUU Da Gwamnati Kan Yajin Aikin ASUU Kuwa?

by Sallau Kaisi Dauda
9 months ago
in Kananan Labarai
0
Shin Dalibai Na Da Wakilai A Tattaunawa Tsakanin ASUU Da Gwamnati Kan Yajin Aikin ASUU Kuwa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ni ban san ma ina shugabanni Kungiyar Daliban Jami’o’in ta Kasa (NANS) da na jihohi suka shiga tun a lokacin da aka fara yajin aikin da ya ki ci ya ki cinyewa tsakanin ASUU da Gwamnatin Tarayya.

Shin suna ma raye kuwa? Shin suna ma da wakilai a cikin kwamitin da ake zaman tattaunawa tsakanin Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) da Gwamnatin tarayya?

  • Sai Mun Yi Gwajin Miyagun Kwayoyi Kafin Daura Aure A Abuja – NDLEA
  • APC Ta Dunkule Kan Tinubu, PDP Na Kokarin Sulhu Da Wike

Idan suna da su, ina su ke? Mai suka ce? Idan ba su da wakilai a zaman. To mai ya sa? Dole ya kamata a ce dalibai na da wakilci cikin zaman, domin lamarin ya shafe bangarori uku ne; ASUU, Gwamnatin Tarayya da kuma dalibai, saboda haka ya kamata kowa na da wakilci a zaman.

Gwamnati da wakilai dalibai kowa ya mallaki duk takardun bukatun ASUU, ta nan ne su daliban za su fahimci ina aka nufa.

Mai gwamnati ta ce za ta yi, mai ta ce ba za ta yi ba. Amma matukar dalibai basu da wakilai a cikin zaman, to cikin duhu za su kasance ko da yaushe. Domin ko an janye yajin aikin za a sa ke komawa.

Labarai Masu Nasaba

NIS Ta Kalubalanci ‘Yan Jarida Kan Bayar Da Rahotannin Tafiye-tafiyen Kasashen Waje

Kwanturolan NIS Reshen Ribas Ya Nemi Kara Inganta Kwazon Kwararrun ‘Yan Nijeriya

Domin bana ganin kaman shugabannin kungiyar dalibai na taimaka wa daliban yadda ya kamata domin kawo karshen wannan yajin aikin na ASUU.

Matakai da shugabannin kungiyar daliban suke dauka bai gamsar da ni kamar suna yi wa daliban shugabanci yadda ya kamata ba.

Kamata ya yi yadda mu ke ganin shugabannin ASUU da na Gwamnatin Tarayya kullum cikin gidan talabijin da jaridu, su ma a dinga ganin su haka muna jin inda suka dosa da sauransu kan lamarin.

Domin su za su matsa wa ASUU da gwamnati su yi abin da ya kamata. Idan kai da abu ya shafe ka kai tsaye baka nuna ka damu ba, to ina kuma ga wani daban?

Wannan yajin aikin ASUU ba wanda bai shafa ba, amma kai tsaye ta fi shafar daliban Jami’a. Saboda haka su ya kamata a fi jin su a ko da yaushe, amma shiru kake ji.

Na fahimci da ASUU da gwamnati kowa na da maganar banza a bakin shi. Idan fa har da gaske suke yi, to dole ASUU da gwamnati su daina fitowa suna jefa wa juna maganganun banza wanda bai dace ba. Sannan su daina fito da abin da da suka tattauna a zaman da suke yi har sai sun samu matsaya.

Saboda ‘yan jaridu da wadansu mutane na kara rura wutar yakin da ke tsakanin ASUU da gwamnati.

Su kuma shugabannin kungiyar daliban jami’a kamar ba sa raye a duniya. Dole su ma za su matsa wa ASUU da gwamnati su yi abin da ya kamata. Idan ba su da wakilai a zaman da ake yi, su nema dole suma a sa su cikin zaman.

Tags: ASUUDalibaiGwamnatin TarayyaKungiyar DalibaiNANSRa'ayiShugabanciWakilciYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sai Mun Yi Gwajin Miyagun Kwayoyi Kafin Daura Aure A Abuja – NDLEA

Next Post

Kasurgumin Dan Bindiga ‘Bello Turji’ Ya Rungumi Zaman Lafiya, Ya Koma Yakar ‘Yan Bindiga – Gwamnati

Related

NIS Ta Kalubalanci ‘Yan Jarida Kan Bayar Da Rahotannin Tafiye-tafiyen Kasashen Waje
Labarai

NIS Ta Kalubalanci ‘Yan Jarida Kan Bayar Da Rahotannin Tafiye-tafiyen Kasashen Waje

1 week ago
Kwanturolan NIS Reshen Ribas Ya Nemi Kara Inganta Kwazon Kwararrun ‘Yan Nijeriya
Labarai

Kwanturolan NIS Reshen Ribas Ya Nemi Kara Inganta Kwazon Kwararrun ‘Yan Nijeriya

2 weeks ago
Gwamnati Ta Amince Da Sabbin Manufofin Bunkasa Samar Da Motoci A Nijeriya 
Labarai

Gwamnati Ta Amince Da Sabbin Manufofin Bunkasa Samar Da Motoci A Nijeriya 

3 weeks ago
Shugaban NIS Ya Nemi Birtaniya Ta Rika Mutunta Bakin Hauren Nijeriya
Kananan Labarai

Shugaban NIS Ya Nemi Birtaniya Ta Rika Mutunta Bakin Hauren Nijeriya

3 weeks ago
Hukumar KTSTA Ta Ƙaddamar Da Sabbin Motocin Sufuri A Katsina
Labarai

Hukumar KTSTA Ta Ƙaddamar Da Sabbin Motocin Sufuri A Katsina

2 months ago
An Nada Sabbin Shugabannin Hisbah A Jihar Katsina
Kananan Labarai

An Nada Sabbin Shugabannin Hisbah A Jihar Katsina

2 months ago
Next Post
Kasurgumin Dan Bindiga ‘Bello Turji’ Ya Rungumi Zaman Lafiya, Ya Koma Yakar ‘Yan Bindiga – Gwamnati

Kasurgumin Dan Bindiga 'Bello Turji' Ya Rungumi Zaman Lafiya, Ya Koma Yakar 'Yan Bindiga - Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Da Dumi-dumi: Hukumar DSS Ta Yi Wa Ofishin EFCC Kawanya, Ta Hana Jami’an Shiga Ginin

Da Dumi-dumi: Hukumar DSS Ta Yi Wa Ofishin EFCC Kawanya, Ta Hana Jami’an Shiga Ginin

May 30, 2023
Yadda Amurka Ta Yi Kokarin Amfani Da Nukiliya Wajen Tarwatsa Wata

Yadda Amurka Ta Yi Kokarin Amfani Da Nukiliya Wajen Tarwatsa Wata

May 30, 2023
Gwamnatin Kano Za Ta Sake Bude Shari’ar Zargin Kisan Da Ake Yi Wa Alhassan Doguwa 

Gwamnatin Kano Za Ta Sake Bude Shari’ar Zargin Kisan Da Ake Yi Wa Alhassan Doguwa 

May 30, 2023
Sabon Gwamnan Kano Ya Kori Shugaban Hukumar Alhazai Na Jihar Da Wasu

Sabon Gwamnan Kano Ya Kori Shugaban Hukumar Alhazai Na Jihar Da Wasu

May 30, 2023
Kamfanin NNPCL Ya Goyi Bayan Cire Tallafin Man Fetur, Ya Yi Alkawarin Samar Da Wadataccen Mai

Kamfanin NNPCL Ya Goyi Bayan Cire Tallafin Man Fetur, Ya Yi Alkawarin Samar Da Wadataccen Mai

May 30, 2023
Kasar Sin Ta Tuntuba Tare Da Musayar Ra’ayi Da Dukkan Bangarori Game Da Warware Rikicin Ukraine A Siyasance

Kasar Sin Ta Tuntuba Tare Da Musayar Ra’ayi Da Dukkan Bangarori Game Da Warware Rikicin Ukraine A Siyasance

May 29, 2023
Sin Da Afirka Sun Fi Bukatar Kara Hadin Gwiwa Da Juna

Sin Da Afirka Sun Fi Bukatar Kara Hadin Gwiwa Da Juna

May 29, 2023
Tinubu Ya Taya Erdoğan Murnar Nasarar Cin Zaben Shugaban Kasar Turkiyya

Tinubu Ya Taya Erdoğan Murnar Nasarar Cin Zaben Shugaban Kasar Turkiyya

May 29, 2023
Sabon Gwamnan Sakkwato Ahmed Aliyu Ya Nemi Goyon Bayan ‘Yan Adawa A Jihar

Sabon Gwamnan Sakkwato Ahmed Aliyu Ya Nemi Goyon Bayan ‘Yan Adawa A Jihar

May 29, 2023
An Wallafa Littafi Kan Jawabin Shugaba Xi Jinping A Wajen Taron Kolin Kasar Sin Da Yankin Tsakiyar Asiya

An Wallafa Littafi Kan Jawabin Shugaba Xi Jinping A Wajen Taron Kolin Kasar Sin Da Yankin Tsakiyar Asiya

May 29, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.