ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Dalibai Na Da Wakilai A Tattaunawa Tsakanin ASUU Da Gwamnati Kan Yajin Aikin ASUU Kuwa?

by Sallau Kaisi Dauda
4 years ago
ASUU

Ni ban san ma ina shugabanni Kungiyar Daliban Jami’o’in ta Kasa (NANS) da na jihohi suka shiga tun a lokacin da aka fara yajin aikin da ya ki ci ya ki cinyewa tsakanin ASUU da Gwamnatin Tarayya.

Shin suna ma raye kuwa? Shin suna ma da wakilai a cikin kwamitin da ake zaman tattaunawa tsakanin Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) da Gwamnatin tarayya?

  • Sai Mun Yi Gwajin Miyagun Kwayoyi Kafin Daura Aure A Abuja – NDLEA
  • APC Ta Dunkule Kan Tinubu, PDP Na Kokarin Sulhu Da Wike

Idan suna da su, ina su ke? Mai suka ce? Idan ba su da wakilai a zaman. To mai ya sa? Dole ya kamata a ce dalibai na da wakilci cikin zaman, domin lamarin ya shafe bangarori uku ne; ASUU, Gwamnatin Tarayya da kuma dalibai, saboda haka ya kamata kowa na da wakilci a zaman.

ADVERTISEMENT

Gwamnati da wakilai dalibai kowa ya mallaki duk takardun bukatun ASUU, ta nan ne su daliban za su fahimci ina aka nufa.

Mai gwamnati ta ce za ta yi, mai ta ce ba za ta yi ba. Amma matukar dalibai basu da wakilai a cikin zaman, to cikin duhu za su kasance ko da yaushe. Domin ko an janye yajin aikin za a sa ke komawa.

LABARAI MASU NASABA

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

Domin bana ganin kaman shugabannin kungiyar dalibai na taimaka wa daliban yadda ya kamata domin kawo karshen wannan yajin aikin na ASUU.

Matakai da shugabannin kungiyar daliban suke dauka bai gamsar da ni kamar suna yi wa daliban shugabanci yadda ya kamata ba.

Kamata ya yi yadda mu ke ganin shugabannin ASUU da na Gwamnatin Tarayya kullum cikin gidan talabijin da jaridu, su ma a dinga ganin su haka muna jin inda suka dosa da sauransu kan lamarin.

Domin su za su matsa wa ASUU da gwamnati su yi abin da ya kamata. Idan kai da abu ya shafe ka kai tsaye baka nuna ka damu ba, to ina kuma ga wani daban?

Wannan yajin aikin ASUU ba wanda bai shafa ba, amma kai tsaye ta fi shafar daliban Jami’a. Saboda haka su ya kamata a fi jin su a ko da yaushe, amma shiru kake ji.

Na fahimci da ASUU da gwamnati kowa na da maganar banza a bakin shi. Idan fa har da gaske suke yi, to dole ASUU da gwamnati su daina fitowa suna jefa wa juna maganganun banza wanda bai dace ba. Sannan su daina fito da abin da da suka tattauna a zaman da suke yi har sai sun samu matsaya.

Saboda ‘yan jaridu da wadansu mutane na kara rura wutar yakin da ke tsakanin ASUU da gwamnati.

Su kuma shugabannin kungiyar daliban jami’a kamar ba sa raye a duniya. Dole su ma za su matsa wa ASUU da gwamnati su yi abin da ya kamata. Idan ba su da wakilai a zaman da ake yi, su nema dole suma a sa su cikin zaman.

ASUU
Sallau Kaisi Dauda
+ postsBio

    MASU ALAKA

    MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi
    Addini

    MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

    May 2, 2026
    Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya
    Kananan Labarai

    Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

    April 28, 2026
    Wakili Ya Rasu Kwana 3 Da Karewar Wa’adinsa A Matsayin Dan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi
    Kananan Labarai

    2027: Majalisar Dattawa Za Ta Ɗage Zaman Ta A Ranar Alhamis Saboda Zaɓen Fidda Gwani

    April 28, 2026
    Next Post
    Kasurgumin Dan Bindiga ‘Bello Turji’ Ya Rungumi Zaman Lafiya, Ya Koma Yakar ‘Yan Bindiga – Gwamnati

    Kasurgumin Dan Bindiga 'Bello Turji' Ya Rungumi Zaman Lafiya, Ya Koma Yakar 'Yan Bindiga - Gwamnati

    LABARAI MASU NASABA

    Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

    Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

    July 15, 2026
    Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

    Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

    July 15, 2026
    ‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

    ‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

    July 15, 2026
    ‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

    ‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

    July 15, 2026
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

    July 14, 2026
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

    July 14, 2026
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

    July 14, 2026
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

    July 14, 2026
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

    July 14, 2026
    Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

    Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

    July 14, 2026

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

    No Result
    View All Result
    • Gida
    • Labarai
      • Manyan Labarai
      • Kananan Labarai
      • Masarautu
      • Bakon Marubuci
      • Dausayin Musulunci
      • Daga Kasar Sin
      • Nishadi
      • Noma Da Kiwo
      • Sana’a Sa’a
      • Tambarin Dimokuradiyya
      • Taskira
      • Daga Birnin Sin
      • Ado Da Kwalliya
    • Siyasa
    • Wasanni
    • Al’adu
    • Al’ajabi
    • Labaran Kasuwanci
    • Karanta cikin Turanci

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.