• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kawancen Yakar APC: Jam’iyyun Adawa Sun Shiga Dimuwa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga dukkan alamu yunkurin da jam’iyyun adawa ke yi na yin kawance domin yakar jam’iyya mai Mulki ta APC ya shiga garari, yayin da wasu manyan jam’iyyun adawa suka nesanta kansu da lamarin.

A ranar Alhamis 7 ga Disambar 2023, wasu rahotanni sun yi nuni da cewa akwai wasu jam’iyyun adawa su 7 da suke kokarin yin kawancen siyasa domin fatattakar jam’iyyar APC daga kan maragar mulkin Nijeriya.
Gamayyar jam’iyyun sun kunshi PDP da ADC da SDP da PAM da NNPP da YPP da kuma ZLP.

  • Ministan Wajen Angola: Manyan Ababen More Rayuwa Da Kamfanonin Sin Suka Gina A Kasar Angola Sun Inganta Ci Gaban Kasar

Taron hadin kan sun yi ne da nufin yakar jam’iyya mai mulki ta APC, wanda rahotanni ya nuna cewa shugabannin jam’iyyun ne suka yi wannan taron a babban hedikwatan jam’iyyar SDP da ke Abuja.

Shugaban jam’iyyar SDP na kasa, Shehu Gabam ya ce jam’iyyun sun gaji matuka kan yadda yanayin kasar nan yake a birkice, babu wani abu da ke tafiya daidai, musamman yadda ake samun rudani a shari’u da aka yi na gwamnoni kanar a jihohin Zamfara da Nasarawa da Kano da Filato.

Jami’iyyun adawa dai sun yi rashin nasara a kotuna a wadannan jihohin bayan da hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta ayyanasu a matsayin wadanda suka yi nasara.
Bayanai dai na nuna cewa babbar jam’iyyar adawa a Najeriya ta PDP ta sami wakilci a taron, inda mai rikon mukamin sakataren jam’iyyar na kasa, Senonji Koshedo ya wakilci mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Umar Damagum.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

A cewar shugabannin jam’iyyun adawar dai, babban dalilin wannan hadin kan shi ne a tabbatar da ingancin dimokuradiyya a Nijeriya ta hanayar samun jam’iyyar adawa mai karfin gaske da za ta iya tunkarar jam’iyya mai mulki.

Amma kuma wasu bayanai na nuna cewa kawancen da aka yi bai kai ga yin maja ba, ma’ana jam’iyyun siyasar za su kasance a matsayinsu na jam’iyyu masu zaman kansu ko da za su yi aiki tare don kawar da APC.
Ko da yake wasu na ganin cewa wannan kawance nasu ba mai yiwuwa ba ne don kowa manufarsa daban. Sanin kowa ne sai hali ya zo daya ake abota.

Haka kuma wasu bayanan na nuna cewa wasu wakilan jam’iyyun da suka halarci taron sun je ne a karin kansu ba da yawun jam’iyyunsu ba.
Duk da yake mai rikon sakataren jam’iyyar PDP na kasa, Koshoedo ya halarci taron ya kuma nuna goyon bayansa a taron, amma jam’iyyar PDP ta nesanta kanta da hadin gwiwar. Sakataren watsa labaran PDP, Debo Ologunagba, ya musanta shiga tattaunawar yin kawance da jam’iyyun adawan guda shida.

Ita ma a nata bangaren, kwamitin gudanarwa na jam’iyyar NNPP ya nesanta kansa da shiga tattaunawar kawance da wasu jam’iyyun adawa. Jam’iyyar NNPP ta kasa ta bayyana haka ne a wata sanarwa da mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Abba Ali, ya fitar a birnin tarayya Abuja. Ya ce NNPP ba ta daga cikin mambobin gamayyar jam’iyyun da suka cure wuri daya domin yin kawance.

Sanarwar ta ce, “An jawo hankalin shugabancin jam’iyya kan wasu rahotannin da jaridu suka wallafa cewa an kafa gamayyar jam’iyyu kuma ta kunshi NNPP da wasu jam’iyyun siyasa.”
“Muna mai farin cikin sanar da cewa babu wani abu makamancin haka. Rahoton wanda ya watsu ranar Jumu’a, 8 ga watan Satumba, 2023 ya nuna cewa NNPP, PDP da wasu jam’iyyu sun yi kawance.”

Ali ya kara da cewa tun bayan zaben 2023, babu wani mamban NNPP da ya zauna da wata jam’iyya ko tawaga ko daidaiku da nufin tattaunawar kawance.

Jam’iyyar LP sun barranta kansu da shiga wannan hadaka kamar yadda mai magana da yawun jam’iyyar, Obiora Ifoh ya bayyana. Ya ce ba da su ba, don ba a kama hanyar hadin kai ba. ya ce idan za su yi hadaka za su duba tanaje-tanajen dokokin zabe da ya samar a kan hadaka.

Alamu dai na nuna cewa gamayyar jam’iyyun adawa ba su tsara ainihin yadda za a yi hadakar ba, duk da yake sakataren hadakar jam’iyyun, Willy Ezugwu ya ce hadakarsu na jam’iyyu masu rajista a Nijeriya ne, don haka ba suna karkashin wani ba ne da za su amsa sunansa.

Abun da kowa zai duba shi ne, hannu daya ba ya daukan jinka, kuma idan ana neman samun nasara a kowani abu dole ne a hadu waje guda don a sami nasarar, kamar abun da ya faru a shekarar 2014 inda jam’iyyun adawa suka hadu suka kafa jam’iyyar APC wanda ta sami nasara a zaben shekarar 2015.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCLPPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Kungiyar USCBC

Next Post

Gwamnonin Arewa Sun Bada Tallafin Naira Miliyan 180 Ga Al’ummar Tudun biri

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 week ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Gwamnonin Arewa Sun Bada Tallafin Naira Miliyan 180 Ga Al’ummar Tudun biri

Gwamnonin Arewa Sun Bada Tallafin Naira Miliyan 180 Ga Al'ummar Tudun biri

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.