ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kawancen Yakar APC: Jam’iyyun Adawa Sun Shiga Dimuwa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
APC

Ga dukkan alamu yunkurin da jam’iyyun adawa ke yi na yin kawance domin yakar jam’iyya mai Mulki ta APC ya shiga garari, yayin da wasu manyan jam’iyyun adawa suka nesanta kansu da lamarin.

A ranar Alhamis 7 ga Disambar 2023, wasu rahotanni sun yi nuni da cewa akwai wasu jam’iyyun adawa su 7 da suke kokarin yin kawancen siyasa domin fatattakar jam’iyyar APC daga kan maragar mulkin Nijeriya.
Gamayyar jam’iyyun sun kunshi PDP da ADC da SDP da PAM da NNPP da YPP da kuma ZLP.

  • Ministan Wajen Angola: Manyan Ababen More Rayuwa Da Kamfanonin Sin Suka Gina A Kasar Angola Sun Inganta Ci Gaban Kasar

Taron hadin kan sun yi ne da nufin yakar jam’iyya mai mulki ta APC, wanda rahotanni ya nuna cewa shugabannin jam’iyyun ne suka yi wannan taron a babban hedikwatan jam’iyyar SDP da ke Abuja.

ADVERTISEMENT

Shugaban jam’iyyar SDP na kasa, Shehu Gabam ya ce jam’iyyun sun gaji matuka kan yadda yanayin kasar nan yake a birkice, babu wani abu da ke tafiya daidai, musamman yadda ake samun rudani a shari’u da aka yi na gwamnoni kanar a jihohin Zamfara da Nasarawa da Kano da Filato.

Jami’iyyun adawa dai sun yi rashin nasara a kotuna a wadannan jihohin bayan da hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta ayyanasu a matsayin wadanda suka yi nasara.
Bayanai dai na nuna cewa babbar jam’iyyar adawa a Najeriya ta PDP ta sami wakilci a taron, inda mai rikon mukamin sakataren jam’iyyar na kasa, Senonji Koshedo ya wakilci mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Umar Damagum.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

A cewar shugabannin jam’iyyun adawar dai, babban dalilin wannan hadin kan shi ne a tabbatar da ingancin dimokuradiyya a Nijeriya ta hanayar samun jam’iyyar adawa mai karfin gaske da za ta iya tunkarar jam’iyya mai mulki.

Amma kuma wasu bayanai na nuna cewa kawancen da aka yi bai kai ga yin maja ba, ma’ana jam’iyyun siyasar za su kasance a matsayinsu na jam’iyyu masu zaman kansu ko da za su yi aiki tare don kawar da APC.
Ko da yake wasu na ganin cewa wannan kawance nasu ba mai yiwuwa ba ne don kowa manufarsa daban. Sanin kowa ne sai hali ya zo daya ake abota.

Haka kuma wasu bayanan na nuna cewa wasu wakilan jam’iyyun da suka halarci taron sun je ne a karin kansu ba da yawun jam’iyyunsu ba.
Duk da yake mai rikon sakataren jam’iyyar PDP na kasa, Koshoedo ya halarci taron ya kuma nuna goyon bayansa a taron, amma jam’iyyar PDP ta nesanta kanta da hadin gwiwar. Sakataren watsa labaran PDP, Debo Ologunagba, ya musanta shiga tattaunawar yin kawance da jam’iyyun adawan guda shida.

Ita ma a nata bangaren, kwamitin gudanarwa na jam’iyyar NNPP ya nesanta kansa da shiga tattaunawar kawance da wasu jam’iyyun adawa. Jam’iyyar NNPP ta kasa ta bayyana haka ne a wata sanarwa da mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Abba Ali, ya fitar a birnin tarayya Abuja. Ya ce NNPP ba ta daga cikin mambobin gamayyar jam’iyyun da suka cure wuri daya domin yin kawance.

Sanarwar ta ce, “An jawo hankalin shugabancin jam’iyya kan wasu rahotannin da jaridu suka wallafa cewa an kafa gamayyar jam’iyyu kuma ta kunshi NNPP da wasu jam’iyyun siyasa.”
“Muna mai farin cikin sanar da cewa babu wani abu makamancin haka. Rahoton wanda ya watsu ranar Jumu’a, 8 ga watan Satumba, 2023 ya nuna cewa NNPP, PDP da wasu jam’iyyu sun yi kawance.”

Ali ya kara da cewa tun bayan zaben 2023, babu wani mamban NNPP da ya zauna da wata jam’iyya ko tawaga ko daidaiku da nufin tattaunawar kawance.

Jam’iyyar LP sun barranta kansu da shiga wannan hadaka kamar yadda mai magana da yawun jam’iyyar, Obiora Ifoh ya bayyana. Ya ce ba da su ba, don ba a kama hanyar hadin kai ba. ya ce idan za su yi hadaka za su duba tanaje-tanajen dokokin zabe da ya samar a kan hadaka.

Alamu dai na nuna cewa gamayyar jam’iyyun adawa ba su tsara ainihin yadda za a yi hadakar ba, duk da yake sakataren hadakar jam’iyyun, Willy Ezugwu ya ce hadakarsu na jam’iyyu masu rajista a Nijeriya ne, don haka ba suna karkashin wani ba ne da za su amsa sunansa.

Abun da kowa zai duba shi ne, hannu daya ba ya daukan jinka, kuma idan ana neman samun nasara a kowani abu dole ne a hadu waje guda don a sami nasarar, kamar abun da ya faru a shekarar 2014 inda jam’iyyun adawa suka hadu suka kafa jam’iyyar APC wanda ta sami nasara a zaben shekarar 2015.

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

APC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Gwamnonin Arewa Sun Bada Tallafin Naira Miliyan 180 Ga Al’ummar Tudun biri

Gwamnonin Arewa Sun Bada Tallafin Naira Miliyan 180 Ga Al'ummar Tudun biri

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.