• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kenya Ta Dakatar Da Yi Wa Ma’aikatan Gwamnati Karin Albashi

bySadiq
1 year ago
Kenya

Hukumar Albashi da Jin Dadin Ma’aikata ta Kenya, ta janye shirinta na kara albashin ‘yan siyasa masu rike da madafun iko daga 1 ga watan Yuli.

Kenya ta dakatar da shirinta na kara albashin ‘yan siyasa masu rike da madafun iko daga 1 ga watan Yuli.

  • NDLEA Ta Bayar Da Shawarar Tilasta Wa Ma’aurata Yin Gwajin Shan Ƙwaya A Kano
  • Tinubu Zai Halarci Zikirin Juma’a A Fadar Aminu Ado Ta Nassarawa

A ranar Laraba ne Hukumar Kula da Albashi da Jindadin Ma’aikata ta bayyana cewa ta “dakatar da shirin kara albashin dukkanin ‘yan siyasa masu rike da madafun iko, kuma za ta yi duba ga shawara kan albashin dukkanin ‘yan siyasa don tabbatar dorewar kashe kudade.”

Shugabar Hukumar Lyn Mengich ta ce an yanke hukuncin dakatar da shirin karin albashin ne bayan tattaunawa da neman shawarwarin jama’a.

Hukumar ta SRC ta fitar da wata sanarwa a hukumance a jaridar Gwamnatin Kenya a watan Agustan 2023 inda ta bayyana shirinta na ƙara albashin ‘yan siyasa masu rike da madafun iko daga 1 ga Yulin 2024.

LABARAI MASU NASABA

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

‘Mu rayu daidai gwargwadon arzikinmu’

Shugaban Kasar Kenya William Ruto ya umarci Ma’aikatar Kudi ta kasa da ta dakatar da shirin karin albashin.

Shugaba Ruto ya ce wannan mataki zai taimaka wa Kenya ‘Ta rayu daidai gwagwardon arzikinta”.

Kungiyar gwamnoni, wadda ta kunshi dukkan gwamnoni 47 na kasar Kenya, ta yi kira ga Hukumar SRC da ta dakatar da shirin karin albashin ‘yan siyasa masu rike da madafun iko.

Sabon tsarin albashin da aka kawo ya tanadi cewa dan majalisar dokoki zai dinga karbar kudin Kenya 739,600 kwatankwancin dalar Amurka 5,730 a kowanne wata, kari kan ksh 725,500 kwatankwacin dala 5,620 da suke karba a halin yanzu.

Almubazzaranci a gwamnati

Sabon albashin gwamnoni zai kama ksh 990,000 ($7,620), daga 957,000 ($7,420) da suke karba a yanzu.

Ministoci kuma da suke da matsayi iri daya da na gwamnonin za su samu kari kwatankwacin na gwamnonin.

Kenya na da ministoci 22.

Karin albashin zai janyo kenya ta kashe kusan Sulallan kasar biliyan 11 (dala miliyan $85.3) a kowacce shekara, kamar yadda jaridar ƙasa ta Kenya ta rawaito a ranar Laraba.

Matakin janye karin albashin ‘yan siyasar ya zo ne a lokacin da ‘yan kasar ke kira ga gwamnatin Ruto da ta kawo karshen almubazzaranci a cikin gwamnati.

Zanga-angar adawa da karin haraji da aka yi a baya-bayan nan a Kenya ta janyo asarar rayukan mutum 39, kamar yadda Hukumar Kare Hakkokin Dan’adam ta Kenya mallakin gwamnati ta sanar.

Zanga-zangar ta sanya Ruto janye Dokar Kudade ta 2024, wadda ta tanadi kara yawan haraji a kasar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?
Kasashen Ketare

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?
Kasashen Ketare

Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

September 28, 2025
Next Post
Kotu Ta Dage Shari’ar Matashin Da Ya Kone Masallata A Kano

Kotu Ta Dage Shari'ar Matashin Da Ya Kone Masallata A Kano

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version