• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kirsimati: ‘Yan Nijeriya 163,000 Suka Ci Gajiyar Tallafin Sufurin Gwamnati – Minista

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
minista

Shugaban kwamitin aiwatar da shirin tallafin sufuri na karshen shekara na Shugaba Bola Tinubu, Dakta Dele Alake, ya bayyana cewa sama da fasinjoji 160,000 ne suka ci gajiyar shirin.

Alake, wanda kuma yake rike da mukamin ministan bunkasa ma’adanai, ya bay-yana hakan ne a cikin rahotonsa da aka gabatar a Jihar Legas.

  • Kirismeti: Kukah Ya Bukaci Tinubu Ya Kawo Karshen Kisan Al’umma
  • Majalisa Ta Amince Tinubu Ya Ciwo Bashin Naira Tiriliyan 7.5

Shirin wanda shugaba Tinubu ya kaddamar a ranar 19 ga watan Disamba ya shafi samar da zirga-zirga kyauta a hanyoyin jiragen kasan Nijeriya (NRC).

Bugu da kari, shugaban kasa ya rage kashi 50 na kudin sufuri ga fasinjojin da ke tafiya a kan hanyoyi 30 da masu gudanar da zirga-zirtar bas a karkashin kungiyar ‘Ludury Bus Owners of Nigeria’ (ALBON).
Da yake bayyana yadda shirin ya gudana, Alake ya jaddada gagarumar nasarar da aka samu.
Ya bayyana cewa ragin sufuri da Shugaba Tinubu ya aiwatar ya samu gagarumar nasara bisa la’akari da yadda ‘yan Nijeriya suka jin dadin lamarin.

“Tun daga ranar 21 ga Disamba zuwa 31 ga Disamba, 2023, alkaluma sun nuna cewa hukumar kula da zirga-zirgar jiragen kasa ta dauki fasinjoji 71,000, yayin da motocin bas da ke aiki a karkashin ALBON sun dauki fasinjoji 77,122.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

“Bas 652 da suka taso daga Oshodi na Legas sun dauki mutum 15,766. Wannan yana nufin cewa fasinjoji 163,878 ne suka amfana daga tallafin sufurin karshen shekara na shugaban kasa a cikin kwanaki 10.
“A yayin da fasinjoji a jirgin kasa suka samu gudanar da zirga-zirga kyautan, san-nan kuma fasinjoji take tafiya a kan hanya suka samu rangwame na kashi 50.”

Alake ya ce shirin na nuni ne da yadda shugaban kasar ke tausayawa da kuma kaunar ’yan Nijeriya wadanda suka kuduri aniyar gudanar da tafiye-tafiye a karshen shekara.

Ministan ya ce shirin yana kuma da nufin rage wa ‘yan kasar matsalar kudi, wadanda a cewarsa suna fuskantar wasu kalubale na tattalin arziki saboda bala’in da duniya ke fama da shi da kuma wasu abubuwan cikin gida.
Ya kara da cewa kwamitin ya dauki wasu matakai na gyara domin magance wasu kurakuran da aka gano wajen aiwatar da shirin, kamar kara wasu hanyoyi guda bi-yu da kuma jawo wasu masu ruwa da tsaki na motocin bas.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
TCN
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
Next Post
Manzon Allah

Allah Ya Daukaka Ambaton Manzon Allah (SAW) A Duniya Da Lahira

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.