• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Allah Ya Daukaka Ambaton Manzon Allah (SAW) A Duniya Da Lahira

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
2 years ago
in Labarai
0
Manzon Allah
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Har yanzu dai muna nan a cikin bayanin irin yabon da Allah (SWT) ya yi wa Annabi (SAW) a cikin Alam nash’rah, ayar da ta ce “mun daukaka ambaton ka”, wato aya ta 4 a cikin surar.

Sahabin Annabi (SAW) Katadatu (RA) ya ce, “Allah ya daukaka ambaton Annabi (SAW) a cikin duniya da kuma lahira. Babu wani mai yin huduba ko mai shaidawa ko sallah face yana fadin cewa na shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Annabi Muhammadu Ma’aikin Allah ne”. Ma’ana a nan, Allah ya daukaka ambaton Annabi ta yadda idan aka fadi sunansa sai a fadi na Annabi (SAW).

  • Sin Ta Sha Alwashin Hadin Gwiwa Da Sauran Sassa Wajen Dakile Tashin Hankali A Tekun Red Sea
  • Yadda ANA Ta Shugabanci Gangamin Saukaka Zuwa Hajjin 2024 A Nijeriya

Abu Sa’idul Kudri (RA), Sahabin Annabi kuma Dan Badar ya ruwaito Annabi (SAW) ya ce “Jibrilu (AS) ya zo mun sai ya ce, Ubangijina kuma Ubangijinka – ya Muhammad – yana cewa shin ka san ma’anar fassarar ayar da ta ce Allah ya daukaka ambatonka? Sai na ce Allah ne da Dan Aikensa (Jibrilu) ya sani. Sai Jibrilu ya ce ma’anar an daukaka ambatonka ita ce Allah ya ce idan aka ambace shi sai a ambace ka tare da shi”.

Ibn Ada’in ya ce ma’anar “mun daukaka ambatonka” tana nufin “Allah ya sanya ambatonsa tare da ambaton Annabi ya zama cikar imani”. Wato idan aka ce “Na shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah”, imani ba zai cika ba dole sai an hada da “Hakika na shaida Muhammadu Manzon Allah ne, (SAW)”.

Ko kuma Ibn Ada’in ya ce a wata ma’anar, ayar tana nufin “Allah ya sanya ambaton Manzon Allah a matsayin ambatonsa”. Wato duk wanda ya ambaci Manzon Allah (Muhammadu) tamkar ya ambaci Allah ne.
Shi ya sa ma wasu Malamai suka ce sunan “Muhammadu” daya ne daga cikin sunayen Allah da ya baiwa Annabi (SAW), kamar yadda ya bashi “Ra’ufu” da “Rahimu”.

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

A wurin Imamu Ja’afarus Sadik (RA) kuma, ma’anar ayar ta “mun daukaka ambatonka tana nufin “Babu wani mutum da zai ambaci Manzon Allah (SAW) da Manzanci face sai ya ambaci Allah, duk kuwa da cewa Allah ne Ubangiji”.

A bangaren wasu malamai kuwa, sun yi nuni da ma’anar ayar zuwa mukamin ceto a ranar Alkiyama. Ranar da kowa zai ce takaina nake yi, sai shi kadai (SAW) zai tashi ya nemi ceto a wurin Allah ya bashi. Kowa sai ya ambace shi a ranar, da Annabawa da mabiyansu kowa zai gaza, Annabi (SAW) kadai ne zai iya. Shi ya sa kowa za a ji yana kiran sunansa (Muhammadu, Muhammadu don godewa) har ma Allah a cikin Alkur’ani yake cewa “Allah zai tsayar da kai a wani bigire abin godewa”.

Haka nan, yana daga daukaka ambaton Annabi (SAW) da Allah ya yi, sa’ilin da ya gwama (hada) bin Manzon Allah a matsayin bin sa (SWT). Allah ya hada sunansa da sunan Annabi (SAW).
Allah yana cewa a cikin Alkur’ani “Ku bi Allah ku bi Manzon Allah daidai-da-daidai (kamar yadda ma’anar wawun na ayar ta nuna)”. A wata ayar kuma ya ce “Ku yi Imani da Allah ku yi Imani da Ma’aikinsa daidai-da-daidai (ita ma wawun din ayar irin ta ayar baya ce, wato ta adafi)”.

Malamai sun ce bai halatta a hada irin wannan magana ba in ba a cikin hakkin Manzon Allah (SAW) ba. Shi kuma tunda Allah ne da kansa ya yi hakan, waye ya isa ya cire?
Malam Alkadiy Iyal ya kawo hadisi wanda ruwayarsa ta daukaka zuwa Sahabin Annabi Khuzaifatul Yamaniy (RA), Manzon Allah (SAW) ya ce “Kar in ji wani dayanku ya ce Allah ya so (wani abu); wane ya so (shi ma, wato a sanya harafin wawun da ke nuna daidai-da-daidai), sai dai mutum ya ce Allah ya so; sannan wane ya so (ma’ana sai da Allah ya so, sannan daga baya wane ya so, ba tare da daidaitawa”. A ka’idar Larabci ba za a yi amfani da “wawun na adafi” ba sai dai harafin “summa”.

Malam Khaddabi ya ce Annabi (SAW) ya shiryar da Sahabbai yin ladabi ga Allah ta yadda sai an gabatar da son Allah sannan a gabatar da son wani (Kamar yadda ya zo a bayanin da muka yi a sama), don haka ne Annabi ya zabar musu amfani da “summa” ma’ana “sannan ko daga baya” domin jera magana da jinkirtawa. Wato sai an fadi na Allah, sannan daga baya a fadi na Bawansa.

Ya zo a wani Hadisi cewa wani mai huduba ya mike a gaban Annabi (SAW) zai yi huduba sai ya ce “Duk wanda ya bi Allah da Ma’aikinsa; ya shiryu, wanda ya saba musu su biyu kuma…” daga nan Annabi (SAW) ya ce “Tir da mai yi ma mutane huduba irin ka, tashi ka tafi”, ma’ana mai hudubar bai iya magana ba.

Abu Sulaiman ya ce Annabi (SAW) ya kyamaci hada sunayen guda biyu (na Allah da nasa) ne da harafin kinaya (jirwaye mai kaman wanka). Amma wani Malamin ya ce ba haka ake nufi ba, ya ce Annabi ya hana ne saboda mai hudubar ya yi wakafi a wurin. Sai dai kuma fahimtar Abu Sulaiman ta fi inganta saboda abin da aka ruwaito a Hadisi Sahihi shi ne mai hudubar bai yi wakafi ba a wurin harafin na kinaya (jirwaye), ya cike maganarsa inda ya ce “wanda ya saba musu su biyu ya halaka”.

Shi kuwa Imamun Nawawi ya ce duk ba haka ba ne. Ya ce sababin da ya sa Annabi (SAW) ya hana irin wannan hadawar saboda a huduba ne ya fada, kuma ita huduba ana so ne a fadi ma’ana wara-wara yadda za a fahimta filla-filla ba a yi kinaya ba. Shi ya sa Annabi (SAW) idan ya fadi wata magana sai ya maimaita don a gane. Amma ba wai ya ki a hada sunayen guda biyu (na Allah da nasa) ba ne. Domin hakan ya zo a cikin Alkur’ani da Hadisi.
Malaman Tafsiri sun yi sabani cikin ma’anar ayar da ke cewa “Allah da Mala’ikunsa “suna” yiwa Annabi salati…”, shin ma’anar “suna salatin” za ta zama a hada Allah Tabaraka Wa Ta’ala da Mala’iku ne cikin yin salatin ko kuma ayar ana kaddarata ce da ma’anar “Allah Yana salati”, “Mala’iku (su ma) suna salati”?.

Wane sashe na malamai sun tafi a kan “Allah Yana salati, Mala’iku suna salati ga Annabi…”, wasu kuma sun kyamaci a ce hakan. Sai suka kaddara fi’ilin (aiki) na “suna” ga Mala’iku bayan sun gabatar da Allah shi kadai Yana salatin a matsayin abin kaddarawa cikin “Yusalluu”, mana “suna”. Alkur’ani yakan kawo irin wannan abin kaddarawan.
To duk fahimtar da mutum ya dauka dai a cikin wadannan ya yi daidai.
Ba gyaran akida ba ne a rika cewa kar a rika ambaton Allah tare da Annabi, a’a, imani ma ba zai cika ba sai an ambaci Allah tare da Annabi (SAW). Shi ya sa ma idan ana neman wani abu ake cewa “don Allah don Manzon Allah”.
An karbo daga Sayyidina Umar bin Khaddab (RA) cewa wata rana yana hira da Manzon Allah (SAW) sai ya ce masa “yana daga fifikonka ya Rasulallahi a wurin Allah, Allah ya sanya bin ka; bin sa ne”.

Allah (SWT) a cikin Alkur’ani, Suratun Nisa’i ya ce “duk wanda ya bi wannan Ma’aiki, ya bi Allah”. A cikin Suratu Ali Imran kuma ya ce “Ka fada musu – ya Rasulallah – in dai kuna son Allah; to ku bi ni sai Allah ya so ku”.
An ruwaito cewa a yayin da wannan ayar ta Ali Imran ta sauka, Kafirai sun ce “Muhammadu yana so ne mutanensa su rike shi Badade kamar yadda Nasara suka riki Isah”. Sai Allah ya saukar da wannan ayar “Gaya musu – ya Rasulallah – ku bi Allah ku bi Ma’aiki (daidai da daidai)”. Allah sai ya daidaita binsa da bin Manzon Allah (SAW) domin ya durmuza hancin Kafiran.

Don haka a cikin addininmu idan Allah ya halatta mana yin abu, don an samu wasu mutanen da ba Musulmi ba suna yi, ba za a kula da su ba ballantana har mutum ya ji shakkun cewa ai tunda wadancan suna yi bai kamata muma mu yi ba. Idan addininmu na Musulunci ya yarda a yi wani abu, to koda Nasara ko Yahudu suna yi; babu ruwanmu da su; ba nasu muke yi ba, na Musulunci muke yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kirsimati: ‘Yan Nijeriya 163,000 Suka Ci Gajiyar Tallafin Sufurin Gwamnati – Minista

Next Post

Burikan ‘Yan Nijeriya A 2024

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

12 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

13 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

15 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

16 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

17 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

18 hours ago
Next Post
Nijeriya

Burikan ‘Yan Nijeriya A 2024

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.