• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

…Ko Goyon Bayan Da Peter Obi Ke Samu Zai Yi Tasiri?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
Obasanjo Ya Zabi Obi A Matsayin Dan Takararsa Na Shugaban Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daidai lokacin da ake haramar hada-hadar zaben 2023, Tsohon Shugaban Kasa, Olusegun Obasanjo ya bayyana goyon bayansa ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi.

A sakon murnar sabowar shekarar 2023 da tsohon shugaban kasa ya rattaba hannu wanda mai taimaka masa, Kehinde Akinyemi ya raba wa ‘yan jarida, Obasanjo ya siffanta Obi a matsayin mabiyinsa, inda ya ce yana goyon bayan tsohon gwamnan Jihar Anambra a zaben 2023.

  • Obasanjo Ya Zabi Obi A Matsayin Dan Takararsa Na Shugaban Kasa

Obasanjo ya ce, “Babu daya daga cikin ’yan takarar da ya zama waliyyi sai idan an kwatanta halinsa da fahimtarsa da iliminsa da da’arsa da kuzarinsa da zai iya kawowa da kokarin da ake bukata na tsayawa a mayar da hankali kan aikin, musamman duba da yadda kasar ta tsinci kanta a halin yanzu da kuma gogewa a kan aikin, ni na zabi Peter Obi a matsayin wanda zan mara wa baya a zaben 2023.

“Saura kamar irinmu duka muna da gudummuwar da za mu iya bayarwa wajen ceto Nijeriya daga yanayin da take ciki na bauta.

“Wani abu mai matukar muhimmanci da zan iya fadi game da Obi shi ne, yana iya aiki da ‘yan arewa da kuma ‘yan kudu matukar ya samu nasarar lashe zabe.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

“Yana da mutanen da za su iya ja masa kunne matukar ya yi ba daidai ba. Shi matashi ne mai jini jika, haka ma mataimakinsa suna da tarin nasarori da suka cimma a rayuwar al’umma da kuma rayuwarsu na kashin kai.”

A wani bangare na wasikar yana cewa, “Ya zama tilas na rubuta wannan wasika ga dukkan ‘yan Nijeriya, musamman ma matsa, abokaina da ke sassa daban-daban na Nijeriya da na duniya, saboda sauke nauyi da kuma muhimmancin hadin gwiwa wajen yanke hukunci ga ‘yan Nijeriya kanana da dattawa kan babban zabe da za a gudanar a kasa da watanni biyu.

“Shekaru bakwai da rabi da suka gabata ba shakka sun kasance shekaru masu tayar da hankali da damuwa ga yawancin ‘yan Nijeriya. Mun tashi daga saman dutse zuwa kwari.

“Shugabanninmu sun yi iya bakin kokarinsu, amma kokarinsu bai zama mafi alheri ga Nijeriya da ‘yan Nijeriya a gida da waje ba. Yawancin ’yan Nijeriya azaba kawai suke sha a duniya.

“Mu da muke raye ya kamata mu gode wa Allah saboda jin kansa, mu jajirce kan sauran ‘yan watannin wannan gwamnati, sannan mu yi addu’a da yin aiki tukuru don samun kyakkyawar makoma nan gaba da kuma samun ‘yanci da muke tsammani.

“Na yi mu’amala da manyan ’yan takarar kuma na ga abin sha’awa a tattare da su ta wata fuskar, kowannensu ya yi ikirarin cewa yana son yin abin da na yi a lokacin shugabancina da kuma mayar da Nijeriya a babban matsayi a cikin dan karamin lokaci na shugabancina.

“Na ji takaicin yadda akasarin su ba su gane cewa a halin da ake ciki Nijeriya ta fara yin kasa ne tun farkon shugabancina a watan Yunin 1999.

“Ko da yake a wancan lokacin, Nijeriya ta kasance cikin mummunan hali kuma tana daf da rugujewa. Ko a wancan lokacin, Nijeriya ba ta fuskanci matsalar rashin tsaro da ya mamaye ko’ina da rashin shugabanci nagari da gudanar da ayyukan ta’addanci da cin hanci da rashawa da rashin incantaccen tattalin arziki da ke haifar da matsanancin talauci da rashin aikin yi da hauhawar farashin kayayyaki kamar na wannan lokaci ba.”

Shi ma shugaban Kungiyar Ijew na kasa, Cif Edwin Clark ya bi sahun Obasanjo wajen mara baya ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Mista Peter Obi domin ya zama shugaban kasan Nijeriya a zaben da zai guda a wata mai zuwa.

Ya ce idan har Obi ya samu daman zama shugaban kasa, za a samu hadin kai a Nijeriya da kuma sake farfado da kasar.
Goyan bayan Clark yana zuwa ne bayan akwanaki uku da Obasanjo ya nuna goyan bayansa ga tsohon gwamnan Jihar Anambra.

Clark ya bayyana cewa ya kamata duk wanda zai zama shugaban kasa ya kasance mai ilimi da kuma gogewa. A cewarsa, ya kamata a bar yankin kudu maso gabas ya fitar da shugaban kasa da zai gaji Shugaban kasa Muhammadu Buhari, saboda yankin yana da masu ilimi da za su iya jagorancin kasar nan.

Haka shi ma gwamnan Jihar Benuwai, Samuel Ortom ya bi sahun Obasanjo wajen mara baya ga Obi a zaben da zai gudana a ranar 25 ga watan Fabrairun 2023.

A cikin wata nasarwa da ya fitar a ranar Talata da ta gabata dauke da sahannun mai taimaka masa a fannin yada labarai, Terber Akase, gwamna ya siffanta Obi a matsayin mutumin da zai iya magance matsalar tattalin arziki, tsaro da kuma sauran matsalolin da ksar nan take fuskanta.

Sai dai kuma mai magana da yawan kwamitin yakin neman zaben APC, Festus Keyamu ya yi watsi da goyon bayan da Obi ke samu a wurin shugabannin yankin kudu. A cewarsa, duk wannan goyon bayan da Obi ke samu ba za su taba yin tasiri ba.

Keyamo ya bayyana hakan ne a shafinsa na Tuwita a ranar Talata.
Keyamo ya kara da cewa Obasanjo da Clerk duk sun goyi bayan Atiku Abubakar a zaben 2019, amma kuma bai kai lamari ba.
Ya ce kuri’un da suka bai wa Atiku a 2019 shi ne suke kokarin bai wa Obi a halin yanzu kuma ba zai kai lamari ba.

Shi kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya bayyana cewa ko kadan bai damu da goyan bayan da Obasanjo da Clark suka yi wa Obi ba. Ya kara da cewa ‘yan Nijeriya ne kadai za su yanke hukunci kan shugaban kasa a 2023.

Da yake zantawa da manema labarai a ranar Talata, kakakin yakin neman zaben Atiku/Okowa, Charles Aniagwu ya bayyana cewa duk da shi Clark ya fito daga Jihar Dalta, jiha daya da mataimakin dan takarar jam’iyyar PDP, Ifeanyi Okowa ba a hana shi fadan ra’ayinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Na Gama Aikina A Turai, Cewar Ronaldo

Next Post

Shari’ar ‘Yar Ganduje: Alkali Ya Umarci ‘Yan Jarida Su Fice Daga Cikin Kotu

Related

Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano
Manyan Labarai

Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

4 hours ago
Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

6 hours ago
Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

8 hours ago
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 
Manyan Labarai

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

11 hours ago
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

13 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

15 hours ago
Next Post
Shari’ar ‘Yar Ganduje: Alkali Ya Umarci ‘Yan Jarida Su Fice Daga Cikin Kotu

Shari'ar 'Yar Ganduje: Alkali Ya Umarci 'Yan Jarida Su Fice Daga Cikin Kotu

LABARAI MASU NASABA

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

August 27, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

August 27, 2025
Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

Yadda Aka Cafke Masu Saka Ƙwayoyi A Jakunkunan Matafiya A Filin Jirgin Sama A Kano

August 27, 2025
Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

August 27, 2025
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

August 27, 2025
Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

August 27, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

August 27, 2025
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

August 27, 2025
Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

August 27, 2025
Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.