• English
  • Business News
Friday, May 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kwankwaso Zai Iya Kai Bantensa?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
kwankwaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan aka duba yanayin siyasa, kowa na iya furta albarkacin bakinsa kan wadanda ake ganin za su iya kai wa ga gaci. Amma ‘yan kafafen yada labarai sun fi kowa zakewa da kokarin nuna cewa gwaninsu ne a kan gaba. Sai dai kuma wasu daga cikin ‘yan kungiyar Kwankwasiyya suna wuce gona da iri, musamman wadanda ba sa goyon bayansu da gwaninsu.

A 2019, jama’a sun nuna goyon bayan Tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Masu Kwankwaso ne ba don mutanensa sai don an yi na’am da kudirorinsa. Kuma har yau akwai wadanda ba su da wani zabi wajen zabar shugaban Nijeriya sai Kwankwaso saboda, kwarewa, kuzari, da aiki musamman na gina ilmi da ya bai wa matasa, sai dai kuma Allah ne mai bayar da mulki ga wanda yake so, lallai Allah na iya ba shi yana kuma iya hana shi.

  • Gwamnatin Tarayya Ba Ta Muhimmanta Tsaro Ba – Matawalle

Amma a rika sara ana duban bakin gatari, idan an ciza kuma a busa wajen yin la’akari da wadannan abubuwan.
A kundin tsarin mulkin Nijeriya ya bayyana ceawa ka’idar lashe zaben shugaban kasa ita ce, lashe akalla kashi a 25 na zabe daga kashi biyu cikin uku na jahohin tarayayyar Nijeriya wato ma’ana jihohi ashirin da hudu.

A lissafin siyasar Nijeriya babi na daya wanda ba a fadi a kundin tsarin mulkin Nijeriya ba, shi ne yankin da dan takara ya fito suke zuba zallar kuri’a, yayin da yankin da ba daga can dan takara yake ba nan ake dambarwar samon kashi 25 zuwa 60.

A wani shafi na lissafin siyasar, ana samo wadannan kuri’un na kashi 25 ne ko ma fiye ta hanyar amfani da karfin ‘ya’yan jam’iyyu masu madafun iko a kowacce jiha kama daga kansila da ‘yan majalisu, kwamishinoni har zuwa gwamna, sannan sarakunan sargajiya da malamai da wasu jagororin al’umma, sai kuma tarin kudi da kan yi taron dangi wa neman wannan kuri’un.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Wani shafin siyasar ya nuna yadda iyalan ‘yan takara kan zamo silar samun kuriunsu, misali, matayansa da kan shiga lungu da sako wajen aminan zumunci da biki su samo musu kuri’ar, wani lokacin ma zamantowar matan wasu kabilu ne da bana dan takara ba ko wasu addinai yana da tasiri, misali Abubakar Atiku me mata hudu masu mabambanta yare kuma kowacce za ta janyo kuri’ar a kabilunta, haka ma Bola Ahmed Tinubu mai mata kirista ko ba komai za ta tsakuro masa kuri’un coci.

Kwarewar dan takara wajen shiga lungu da sako tare da yin amfani da wasu yarukan da ba nasa ba ko da kuwa Turanci ne yana sanya zukatan masu jefa kuri’a, mun ga hakan a siyasar Olusegun Obasanjo ta farko a shekarar 1999.

Zubar da kan dan takara a gaban manyan mutane ba kawai zuwa gaishe su a kekashe ba yana laguda zukatan mabiyan babban mutumin su ji an girmama nasu su ma su girmama ka da kuri’a, na taba halartan wani taro inda na ga malamin da ya yi gayyata na zaune a kan keke da yake yana fama da ciwon kafa, amma shi dan takarar da aka gayyata yana tsaye a kansa babu ko rusunawa ko girmamawa. Nan sai ka ji mabiya na ta Allah wadai da dan takara mai yawan girman kai.

Idan wadancan turakun gaskiya ne suna da tasiri a wanne ‘yan kwankwasiya ke da wani kwarin gwiwa a zaben 2023. Masu iya magana na cewa idan an bi ta barawo a bi ta ma bi sahu.
Akwai abun da ake kira kuri’ar raba gardama, ita wannan kuri’a tana fitowa ne daga wani dan siyasar yanki da kan dage ya kafa wata jam’iyya ya tara mata jama’a da ko da ba za ta iya cin kujerar shugaban kasa da kanta ba za ta iya taimaka wa wani ya ci ta hanyar amfani da wasu dabaru kamar haka;

Ko dai narkewa cikin wata jami’yyar da ke neman cikon kuri’un in ya so sai a yi gyaran fuska akida da manufa su zo daya na wucin gadi, za mu ga milsalin hakan ko kwatankwacinsa a hadewar APC na shekarar 2014.
Ko kuma ta tsaya a gefe guda ta kacaccalawa dan takarar yankin da ta fi kwari kuri’a. Misalin hakan shi ne salon da Tinubu da Malam Shekarau suka yi amfani da shi a 2011, inda suka taimaki Jonathan ya kayar da Buhari, lokacin da Malam Shekaru ya tsaya takarar shugaban kasa a ANPP. Ribadu ya tsaya a ACN, suka lalata alkalla kuri’a milyan 2 da ‘yan kai.
Ita ma wannan siyasar kamar saura tana da amfani da rashin amfaninta, amma amfaninta ya fi yawa su ne kamar hakan;
Samar da isasshen lokaci na gina siyasar cikin yanki da hade yankin guri guda kamar yadda muka ga ACN ta yi a kudu maso yamma.

Samar da shugaban siyasa guda daya maimakon daidaiku masu mabambanta muradu da manufa.
Akwai kuma samar da manhaja da alkibla daya ga yankin a hannun ‘ya’yan yankin da suka san ciwon yankin nasu. Kwato wa yankin wasu makudan hakkoki wadanda idan ba kana da alkalumman kuri’a ba, ba za a ba ka ba, wadannan hakkoki sun hada da ababen more rayuwa, kudin gina siyasa da ilmi da sana’o’i.

Akwai kuma batun samar wa siyasar yankin wasu kujeru na dindindin da ba a isa a hana ba, inda su kuma ba su isa su kasa yi wa wanda ya kai su aiki ba.
Bayan takaitattun wadannan nazari, an ya Kwankwaso zai iya kai bantensa a zaben 2023?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Mu Gamsu Da Yadda Aikin Kwangilar Hanyar Yola Zuwa Mubi Ke Gudana Ba – Gwamnatin Tarayya

Next Post

Rashin Aiki Ga Matasa Ne Silar Tabarbarewar Tsaro A Nijeriya -Bin Imam

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

3 weeks ago
kwankwaso
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

3 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

3 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

4 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

4 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

4 weeks ago
Next Post
imam

Rashin Aiki Ga Matasa Ne Silar Tabarbarewar Tsaro A Nijeriya -Bin Imam

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin

May 22, 2025
Ba Zai Yiwu Amurka Ta Kafawa Chips Kirar Kasar Sin Wani Shinge Ba

Ba Zai Yiwu Amurka Ta Kafawa Chips Kirar Kasar Sin Wani Shinge Ba

May 22, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da ÆŠaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin Æ™amshin Mutuwa – Ganduje

May 22, 2025
Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka

Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka

May 22, 2025
Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

May 22, 2025
Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

May 22, 2025
Za Mu RiÆ™e Wa Minista Tijjani MuÆ™aminsa Bayan HamÉ“arar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Za Mu RiÆ™e Wa Minista Tijjani MuÆ™aminsa Bayan HamÉ“arar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

May 22, 2025
Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

May 22, 2025
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

May 22, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

May 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.