ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kwankwaso Zai Iya Kai Bantensa?

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
kwankwaso

Idan aka duba yanayin siyasa, kowa na iya furta albarkacin bakinsa kan wadanda ake ganin za su iya kai wa ga gaci. Amma ‘yan kafafen yada labarai sun fi kowa zakewa da kokarin nuna cewa gwaninsu ne a kan gaba. Sai dai kuma wasu daga cikin ‘yan kungiyar Kwankwasiyya suna wuce gona da iri, musamman wadanda ba sa goyon bayansu da gwaninsu.

A 2019, jama’a sun nuna goyon bayan Tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Masu Kwankwaso ne ba don mutanensa sai don an yi na’am da kudirorinsa. Kuma har yau akwai wadanda ba su da wani zabi wajen zabar shugaban Nijeriya sai Kwankwaso saboda, kwarewa, kuzari, da aiki musamman na gina ilmi da ya bai wa matasa, sai dai kuma Allah ne mai bayar da mulki ga wanda yake so, lallai Allah na iya ba shi yana kuma iya hana shi.

  • Gwamnatin Tarayya Ba Ta Muhimmanta Tsaro Ba – Matawalle

Amma a rika sara ana duban bakin gatari, idan an ciza kuma a busa wajen yin la’akari da wadannan abubuwan.
A kundin tsarin mulkin Nijeriya ya bayyana ceawa ka’idar lashe zaben shugaban kasa ita ce, lashe akalla kashi a 25 na zabe daga kashi biyu cikin uku na jahohin tarayayyar Nijeriya wato ma’ana jihohi ashirin da hudu.

ADVERTISEMENT

A lissafin siyasar Nijeriya babi na daya wanda ba a fadi a kundin tsarin mulkin Nijeriya ba, shi ne yankin da dan takara ya fito suke zuba zallar kuri’a, yayin da yankin da ba daga can dan takara yake ba nan ake dambarwar samon kashi 25 zuwa 60.

A wani shafi na lissafin siyasar, ana samo wadannan kuri’un na kashi 25 ne ko ma fiye ta hanyar amfani da karfin ‘ya’yan jam’iyyu masu madafun iko a kowacce jiha kama daga kansila da ‘yan majalisu, kwamishinoni har zuwa gwamna, sannan sarakunan sargajiya da malamai da wasu jagororin al’umma, sai kuma tarin kudi da kan yi taron dangi wa neman wannan kuri’un.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Wani shafin siyasar ya nuna yadda iyalan ‘yan takara kan zamo silar samun kuriunsu, misali, matayansa da kan shiga lungu da sako wajen aminan zumunci da biki su samo musu kuri’ar, wani lokacin ma zamantowar matan wasu kabilu ne da bana dan takara ba ko wasu addinai yana da tasiri, misali Abubakar Atiku me mata hudu masu mabambanta yare kuma kowacce za ta janyo kuri’ar a kabilunta, haka ma Bola Ahmed Tinubu mai mata kirista ko ba komai za ta tsakuro masa kuri’un coci.

Kwarewar dan takara wajen shiga lungu da sako tare da yin amfani da wasu yarukan da ba nasa ba ko da kuwa Turanci ne yana sanya zukatan masu jefa kuri’a, mun ga hakan a siyasar Olusegun Obasanjo ta farko a shekarar 1999.

Zubar da kan dan takara a gaban manyan mutane ba kawai zuwa gaishe su a kekashe ba yana laguda zukatan mabiyan babban mutumin su ji an girmama nasu su ma su girmama ka da kuri’a, na taba halartan wani taro inda na ga malamin da ya yi gayyata na zaune a kan keke da yake yana fama da ciwon kafa, amma shi dan takarar da aka gayyata yana tsaye a kansa babu ko rusunawa ko girmamawa. Nan sai ka ji mabiya na ta Allah wadai da dan takara mai yawan girman kai.

Idan wadancan turakun gaskiya ne suna da tasiri a wanne ‘yan kwankwasiya ke da wani kwarin gwiwa a zaben 2023. Masu iya magana na cewa idan an bi ta barawo a bi ta ma bi sahu.
Akwai abun da ake kira kuri’ar raba gardama, ita wannan kuri’a tana fitowa ne daga wani dan siyasar yanki da kan dage ya kafa wata jam’iyya ya tara mata jama’a da ko da ba za ta iya cin kujerar shugaban kasa da kanta ba za ta iya taimaka wa wani ya ci ta hanyar amfani da wasu dabaru kamar haka;

Ko dai narkewa cikin wata jami’yyar da ke neman cikon kuri’un in ya so sai a yi gyaran fuska akida da manufa su zo daya na wucin gadi, za mu ga milsalin hakan ko kwatankwacinsa a hadewar APC na shekarar 2014.
Ko kuma ta tsaya a gefe guda ta kacaccalawa dan takarar yankin da ta fi kwari kuri’a. Misalin hakan shi ne salon da Tinubu da Malam Shekarau suka yi amfani da shi a 2011, inda suka taimaki Jonathan ya kayar da Buhari, lokacin da Malam Shekaru ya tsaya takarar shugaban kasa a ANPP. Ribadu ya tsaya a ACN, suka lalata alkalla kuri’a milyan 2 da ‘yan kai.
Ita ma wannan siyasar kamar saura tana da amfani da rashin amfaninta, amma amfaninta ya fi yawa su ne kamar hakan;
Samar da isasshen lokaci na gina siyasar cikin yanki da hade yankin guri guda kamar yadda muka ga ACN ta yi a kudu maso yamma.

Samar da shugaban siyasa guda daya maimakon daidaiku masu mabambanta muradu da manufa.
Akwai kuma samar da manhaja da alkibla daya ga yankin a hannun ‘ya’yan yankin da suka san ciwon yankin nasu. Kwato wa yankin wasu makudan hakkoki wadanda idan ba kana da alkalumman kuri’a ba, ba za a ba ka ba, wadannan hakkoki sun hada da ababen more rayuwa, kudin gina siyasa da ilmi da sana’o’i.

Akwai kuma batun samar wa siyasar yankin wasu kujeru na dindindin da ba a isa a hana ba, inda su kuma ba su isa su kasa yi wa wanda ya kai su aiki ba.
Bayan takaitattun wadannan nazari, an ya Kwankwaso zai iya kai bantensa a zaben 2023?

kwankwaso
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

kwankwaso
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
imam

Rashin Aiki Ga Matasa Ne Silar Tabarbarewar Tsaro A Nijeriya -Bin Imam

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.