• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Ziyarar Antony Blinken A Kasar Sin Za Ta Banbanta Da Ta Sauran Jami’an Amurka?

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ko Ziyarar Antony Blinken A Kasar Sin Za Ta Banbanta Da Ta Sauran Jami’an Amurka?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yawa daga masu fashin baki na hasashen cewa, mawuyaci ne a samu wani babban sauyi a ziyarar da sakataren wajen Amurka Antony Blinken zai gudanar a kasar Sin, tsakanin ranar Laraba zuwa Jumma’a, musamman duba da cewa an shiga shekarar babban zaben shugabancin Amurka, irin lokacin da abun da kadai ke hade kan manyan jam’iyyun kasar wato Democrat da Republican, shi ne sukar kasar Sin domin jan ra’ayin Amurkawa da samun kuri’u, amma duk da haka, yana da kyau, ganin babban jami’in na Amurka zai gudanar da ziyara a kasar Sin a irin wannan lokaci. 

Haka dai abun yake, idan mun waiwayi ziyarar da sakatariyar cinikayyar Amurka Gina Raimondo ta gudanar a kasar Sin a shekarar bara, da wadda sakatariyar baitul-malin Amurka Janet Yellen ta gudanar a farkon watan nan na Afirilu, da ma dawo da tattaunawa ta kafar bidiyo tsakanin ministocin tsaro na kasashen biyu, wato Lloyd Austin, da takwaran aikinsa na Sin Dong Jun a farkon watan nan.

  • Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?
  • Kasar Sin Na Fatan Amurka Za Ta Girmama Ka’idojin Takara Bisa Adalci

Ko shakka babu, Bahaushe kan ce “Yawan gaisuwa ya fi yawan fada”, wato dai yawan tattaunawa tsakanin sassan biyu, ya fi a ce ana zaman doya da man ja, to amma kuma yawaitar matakan takunkumi kan kamfanonin Sin, da shafawa Sin din kashin kaji da Amurka ke yi, yana bayyana akasin kalaman neman hadin kai da jami’an Amurkan ke furtawa.

Akwai tarin ayyuka da ya dace a gudanar, domin kyautata dangantakar Sin da Amurka, da kuma matakai na kaucewa ci gaba da tabarbarewar alakar tattalin arziki da siyasa tsakanin sassan biyu.

Da farko dai, wajibi ne a yi watsi da batun “Raba Gari”. Kuma hakan zai tabbata ne kawai idan har Amurka ta yi fatali da kokarin danne kamfanonin Sin, irin su babban kamfanin fasahohin sadarwa na Huawei, da fakewa da batun “Tsaron Kasa”, don baiwa kasuwar Amurka kariyar cinikayya, da shawo kan batun haramtawa kamfanonin kirar sassan laturoni na “Chips” na Amurka sayar da hajojin su ga kasuwannin Sin da dai saura su.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Maimakon daukar matakan zargi, da danniya, da kariyar cinikayya da nuna son kai, kamata ya yi Amurka ta hada gwiwa da kasar Sin, da ma sauran kasashen duniya, wajen gina al’umma mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama, ta yadda moriyar bai daya ta dukkanin sassa za ta zarce ta kashin kai. A daya bangaren kuma, nuna fuska biyu, da fada ba cikawa, ba abun da za su haifar illa raba kawuna, da gurgunta amincewa da juna, da lalata moriyar duniya baki daya.( Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Samar Ya Wuce Misali Ko Damuwar Amurka Ta Wuce Kima?

Next Post

Kasar Sin Ta Harba Kumbon Shenzhou-18 Mai Dauke Da ‘Yan Sama Jannati

Related

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal
Daga Birnin Sin

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

1 hour ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

2 hours ago
CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU
Daga Birnin Sin

CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

4 hours ago
Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

5 hours ago
Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

7 hours ago
Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

7 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Harba Kumbon Shenzhou-18 Mai Dauke Da ‘Yan Sama Jannati

Kasar Sin Ta Harba Kumbon Shenzhou-18 Mai Dauke Da ‘Yan Sama Jannati

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

May 16, 2025
Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

May 16, 2025
JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

May 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

May 16, 2025
CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

May 16, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

May 16, 2025
Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

May 16, 2025
Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

May 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.