• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Kofin

Cin kofin nahiyar Afirka gasa ce wacce manyan kasashe suka mamaye shekara da shekaru wajen yawan lashe kofin da kuma yin kokari tun daga farkon gasar har zuwa karshe, sai dai a wannan shekarar ta 2024, ana ganin abin mamaki domin yadda manyan kasashen suke nuna abin kunya sannan kananan kasashe suke ba wa mutane mamaki, yana nuna cewa tabbas kwallon kafa tana canjawa, kuma irin canjin da ya kamata a ce ana gani a wannan nahiyar ta Afirka.

Manyan kasashe ne suka mamaye yawan lashe gasar tun farkon farawa a shekarar 1957 inda kawo yanzu kasar Masar ta lashe gasar sau bakwai, sai kasar Kamaru wadda ta lashe sau biyar sai Ghana mai guda hudu, Nigeria kuma mai guda uku, sannan Kasar Ibory Coast, wadda take karbar bakuncin gasar a wannan lokacin mai guda biyu.

  • An Maido Da Huldar Diplomasyiya Tsakanin Sin Da Nauru, CMG Ta Bude Ofishinta A Nauru
  • Kisan Ummita: Kotu Ta Sanya Ranar 29 Ga Maris Don Yanke Hukunci

Hakan yana nufin manyan kasashen nahiyar Afirka su ne suka mamaye gasar wajen yawan lashewa, amma wannan gasar ta shekara ta 2024 ta zo da abin mamaki kuma masu sharhi akan gasar ta bana suna ganin za’a iya samun canji ganin yadda manyan kasashen suke yin tuntube.

Mai masaukin baki, Ibory Coast na dab da bankwana da gasar, bayan da Ekuatorial Guinea ta dura mata 4-0 ranar Litinin 22 ga watan Janairu, kuma wasa na uku a rukunin farko da suka buga kenan, inda Ekuatorial Guinea ta hada maki bakwai, ita kuwa Ibory Coast maki uku ne da ita sai, Nijeriya ita ma mai maki bakwai wadda take mataki na biyu a cikin rukunin.

 Ibory Coast za ta iya fitowa daga cikin rukuni duk da haka amma za ta jira ko za ta samu zuwa mataki na biyun, bayan da za a dauki tawaga hudu, wadanda suka yi na uku da maki mai yawa saboda tawaga biyu ce daga kowanne rukuni za ta kai zagayen gaba kai tsaye, yayin da za a hada da hudun da suka yi na uku a rukuni, amma wadanda suka hada maki mai yawa.

LABARAI MASU NASABA

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

Wani abin mamaki shi ne bajintar da kasar Cape Berde take yi a gasar, duk da cewa ta fito a cikin rukunin da ya hada kasashen Ghana da kasar Masar da kasar Mozambikue kuma a yanzu haka kasar ta Cape Berde ita ce take jan rukuni na biyu bayan ta hada maki bakwai, sai kasar Masar ta biyu da maki uku, sai Ghana da tuni ta fice daga gasar da maki biyu.

 Tabbas abin mamaki ne a ce Ghana ta fice daga gasar cin kofin nahiyar Afirka a cikin rukuni kuma ta hada maki biyu kacal cikin maki tara da ake ganin za ta iya hadawa kafin fara gasar.

Sai dai tuni hukumomi a kasar ta Ghana suka sanar da korar kociyan tawagar, Chris Hughton, dan Ingila, wanda a baya ya taba koyar da kungiyoyin Newcastle United da Brighton. Har ila yau, hukumar dake kula da kwallon kafa ta Ghana ta sallami ragowar masu ruwa da tsaki a harkar kwallon kafar kasar, sannan nan gaba a cewar su, za su sanar da mataki na gaba da gwamnatin kasar za ta dauka a kan babbar tawagar kasar ta Ghana.

Babban abin mamakin dai shi ne kasar Ibory Coast, kasa mai masaukin baki, wadda ake ganin tana daya daga cikin manyan kasashen da za su iya lashe gasar saboda karfin tawagar sannan bugu da kari a kasar ake bugawa.

Ita ma tawagar ‘yan wasan Super Eagles ta Nijeriya, duk da cewa ta samu tsallakewa zuwa mataki na gaba, amma masu sharhi kan wasanni suna ganin akwai babban aiki a gaban Nijeriya musamman wajen zura kwallo a raga.

 Cikin wasanni uku da Nijeriya ta buga kwallaye uku kacal ta zura a raga, sannan a cikin guda ukun, kwallo guda daya ce kawai Nijeriya ta zura ana cikin wasa domin kwallo daya da bugun fanareti Nijeriya ta zura sai kuma kwallo daya da dan wasan Guinea-Bissau ya ci gida, abin da ake kira da “Own Goal” da turance.

Ita ma Kasar Masar ba ta tabuka abin arziki a gasar ta ba na ba, domin a cikin wasanni uku da kasar ta fafata, ba ta samu nasarar lashe wasa ko guda daya ba, duka wasanninta canjaras ta buga wanda hakan ya sa ta hada maki uku kuma take mataki na biyu a cikin rukunin.

Duk da cewa Senegal ta samu damar tsallakawa matakin wasannin sili daya kwale tun a Juma’ar da ta gabata, amma a wasan da ta fafata ranar Talata tsakaninta da Guinea, ta yi nasara ne da kwallaye 2 da nema wanda ya bata damar kara yawan makinta zuwa 9.

Cikin dukkanin kasashen da suka tsallaka matakin na ‘yan 16 zuwa yanzu dai Ekuatorial Guinea, Najeriya da kuma Cape Berde ne kadai suka kusan kamo Senegal a yawan makin inda dukkaninsu suke da maki bakwai-bakwai.

Yayin da kasashe irinsu Masar suka taki sa a domin kuwa ta zama kasa mafi karancin maki da ta yi nasarar tsallakawa matakin ‘yan 16, lura da cewa ta na da maki 3 ne cal a wasanni 3 da ta buga wanda dukkaninsu ta yi canjaras, ba nasara ba kuma shan kaye.

A daya wasan da aka yi kuwa, Kamaru ta sha da kyar wajen samun gurbi a zagayen kasashe 16 na gasar cin kofin Afrika, bayan nasara kan Gambia da kwallaye 3 da 2 wanda ya ba ta damar kammala wasanninta na rukuni a matsayin ta 2 amma maki guda ita da Guinea wadda ta kammala a matsayin ta 3.

Wannan ne kadai wasan da Kamaru ta iya nasara cikin wasanni 3 da ta doka, wanda ke nuna ita da Guinea wadda ta kammala wasannin rukunin na B a matsayin ta 3 dukkaninsu sun yi nasara a wasa guda ne sun yi canjaras a guda sun kuma sha kaye a guda.

Kafin dai nasarar ta Kamaru, sai da alkalin wasa ya soke kwallo guda da Gambia ta ci, lokacin ana kwallo 3 da 3 kenan tsakanin bangarorin biyu gab da tashi daga wasa, wadda alkalin wasan ya bayyana da ta satar fage.

Duk da cewa Kamarun ta tsallake, amma ita ma Guinea ta yi zaman jiran tsammanin iya shiga sahun kasashen da suka kammala a matsayin na 3 mafiya maki, wato irin dai gurbin da mai masaukin baki Ibory Coast ta jira.

Ibory Coast wadda ke matsayin ta 3 a rukunin A ta kammala ne da maki 3 yayin da bayan nasara a wasa 1 tal da kuma kaye a wasanni 2, wanda ke nuna cewa Guinea na gabanta a yawan maki, domin kuwa ita ta na da maki 4 ne.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru
Wasanni

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu
Manyan Labarai

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

October 25, 2025
Zuwan Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Abuja Ya Nuna Ana Samun Zaman Lafiya A Nijeriya – Matawalle
Wasanni

Zuwan Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Abuja Ya Nuna Ana Samun Zaman Lafiya A Nijeriya – Matawalle

October 25, 2025
Next Post
Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya

Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.