• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cin kofin nahiyar Afirka gasa ce wacce manyan kasashe suka mamaye shekara da shekaru wajen yawan lashe kofin da kuma yin kokari tun daga farkon gasar har zuwa karshe, sai dai a wannan shekarar ta 2024, ana ganin abin mamaki domin yadda manyan kasashen suke nuna abin kunya sannan kananan kasashe suke ba wa mutane mamaki, yana nuna cewa tabbas kwallon kafa tana canjawa, kuma irin canjin da ya kamata a ce ana gani a wannan nahiyar ta Afirka.

Manyan kasashe ne suka mamaye yawan lashe gasar tun farkon farawa a shekarar 1957 inda kawo yanzu kasar Masar ta lashe gasar sau bakwai, sai kasar Kamaru wadda ta lashe sau biyar sai Ghana mai guda hudu, Nigeria kuma mai guda uku, sannan Kasar Ibory Coast, wadda take karbar bakuncin gasar a wannan lokacin mai guda biyu.

  • An Maido Da Huldar Diplomasyiya Tsakanin Sin Da Nauru, CMG Ta Bude Ofishinta A Nauru
  • Kisan Ummita: Kotu Ta Sanya Ranar 29 Ga Maris Don Yanke Hukunci

Hakan yana nufin manyan kasashen nahiyar Afirka su ne suka mamaye gasar wajen yawan lashewa, amma wannan gasar ta shekara ta 2024 ta zo da abin mamaki kuma masu sharhi akan gasar ta bana suna ganin za’a iya samun canji ganin yadda manyan kasashen suke yin tuntube.

Mai masaukin baki, Ibory Coast na dab da bankwana da gasar, bayan da Ekuatorial Guinea ta dura mata 4-0 ranar Litinin 22 ga watan Janairu, kuma wasa na uku a rukunin farko da suka buga kenan, inda Ekuatorial Guinea ta hada maki bakwai, ita kuwa Ibory Coast maki uku ne da ita sai, Nijeriya ita ma mai maki bakwai wadda take mataki na biyu a cikin rukunin.

 Ibory Coast za ta iya fitowa daga cikin rukuni duk da haka amma za ta jira ko za ta samu zuwa mataki na biyun, bayan da za a dauki tawaga hudu, wadanda suka yi na uku da maki mai yawa saboda tawaga biyu ce daga kowanne rukuni za ta kai zagayen gaba kai tsaye, yayin da za a hada da hudun da suka yi na uku a rukuni, amma wadanda suka hada maki mai yawa.

Labarai Masu Nasaba

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Wani abin mamaki shi ne bajintar da kasar Cape Berde take yi a gasar, duk da cewa ta fito a cikin rukunin da ya hada kasashen Ghana da kasar Masar da kasar Mozambikue kuma a yanzu haka kasar ta Cape Berde ita ce take jan rukuni na biyu bayan ta hada maki bakwai, sai kasar Masar ta biyu da maki uku, sai Ghana da tuni ta fice daga gasar da maki biyu.

 Tabbas abin mamaki ne a ce Ghana ta fice daga gasar cin kofin nahiyar Afirka a cikin rukuni kuma ta hada maki biyu kacal cikin maki tara da ake ganin za ta iya hadawa kafin fara gasar.

Sai dai tuni hukumomi a kasar ta Ghana suka sanar da korar kociyan tawagar, Chris Hughton, dan Ingila, wanda a baya ya taba koyar da kungiyoyin Newcastle United da Brighton. Har ila yau, hukumar dake kula da kwallon kafa ta Ghana ta sallami ragowar masu ruwa da tsaki a harkar kwallon kafar kasar, sannan nan gaba a cewar su, za su sanar da mataki na gaba da gwamnatin kasar za ta dauka a kan babbar tawagar kasar ta Ghana.

Babban abin mamakin dai shi ne kasar Ibory Coast, kasa mai masaukin baki, wadda ake ganin tana daya daga cikin manyan kasashen da za su iya lashe gasar saboda karfin tawagar sannan bugu da kari a kasar ake bugawa.

Ita ma tawagar ‘yan wasan Super Eagles ta Nijeriya, duk da cewa ta samu tsallakewa zuwa mataki na gaba, amma masu sharhi kan wasanni suna ganin akwai babban aiki a gaban Nijeriya musamman wajen zura kwallo a raga.

 Cikin wasanni uku da Nijeriya ta buga kwallaye uku kacal ta zura a raga, sannan a cikin guda ukun, kwallo guda daya ce kawai Nijeriya ta zura ana cikin wasa domin kwallo daya da bugun fanareti Nijeriya ta zura sai kuma kwallo daya da dan wasan Guinea-Bissau ya ci gida, abin da ake kira da “Own Goal” da turance.

Ita ma Kasar Masar ba ta tabuka abin arziki a gasar ta ba na ba, domin a cikin wasanni uku da kasar ta fafata, ba ta samu nasarar lashe wasa ko guda daya ba, duka wasanninta canjaras ta buga wanda hakan ya sa ta hada maki uku kuma take mataki na biyu a cikin rukunin.

Duk da cewa Senegal ta samu damar tsallakawa matakin wasannin sili daya kwale tun a Juma’ar da ta gabata, amma a wasan da ta fafata ranar Talata tsakaninta da Guinea, ta yi nasara ne da kwallaye 2 da nema wanda ya bata damar kara yawan makinta zuwa 9.

Cikin dukkanin kasashen da suka tsallaka matakin na ‘yan 16 zuwa yanzu dai Ekuatorial Guinea, Najeriya da kuma Cape Berde ne kadai suka kusan kamo Senegal a yawan makin inda dukkaninsu suke da maki bakwai-bakwai.

Yayin da kasashe irinsu Masar suka taki sa a domin kuwa ta zama kasa mafi karancin maki da ta yi nasarar tsallakawa matakin ‘yan 16, lura da cewa ta na da maki 3 ne cal a wasanni 3 da ta buga wanda dukkaninsu ta yi canjaras, ba nasara ba kuma shan kaye.

A daya wasan da aka yi kuwa, Kamaru ta sha da kyar wajen samun gurbi a zagayen kasashe 16 na gasar cin kofin Afrika, bayan nasara kan Gambia da kwallaye 3 da 2 wanda ya ba ta damar kammala wasanninta na rukuni a matsayin ta 2 amma maki guda ita da Guinea wadda ta kammala a matsayin ta 3.

Wannan ne kadai wasan da Kamaru ta iya nasara cikin wasanni 3 da ta doka, wanda ke nuna ita da Guinea wadda ta kammala wasannin rukunin na B a matsayin ta 3 dukkaninsu sun yi nasara a wasa guda ne sun yi canjaras a guda sun kuma sha kaye a guda.

Kafin dai nasarar ta Kamaru, sai da alkalin wasa ya soke kwallo guda da Gambia ta ci, lokacin ana kwallo 3 da 3 kenan tsakanin bangarorin biyu gab da tashi daga wasa, wadda alkalin wasan ya bayyana da ta satar fage.

Duk da cewa Kamarun ta tsallake, amma ita ma Guinea ta yi zaman jiran tsammanin iya shiga sahun kasashen da suka kammala a matsayin na 3 mafiya maki, wato irin dai gurbin da mai masaukin baki Ibory Coast ta jira.

Ibory Coast wadda ke matsayin ta 3 a rukunin A ta kammala ne da maki 3 yayin da bayan nasara a wasa 1 tal da kuma kaye a wasanni 2, wanda ke nuna cewa Guinea na gabanta a yawan maki, domin kuwa ita ta na da maki 4 ne.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Sin Da Faransa Su Ba Da Jagora Wajen Yin Mu’amala A Shekaru 60 Masu Zuwa

Next Post

Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya

Related

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu
Wasanni

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

1 day ago
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan
Wasanni

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

1 day ago
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal
Wasanni

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

1 day ago
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona
Wasanni

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

3 days ago
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Wasanni

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

5 days ago
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

7 days ago
Next Post
Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya

Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

June 8, 2025
Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

June 8, 2025
Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

June 8, 2025
Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

June 8, 2025
Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

June 8, 2025
Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

June 8, 2025
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

June 8, 2025
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.