• English
  • Business News
Monday, September 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

KOFIN DUNIYA: Za A Kara Yawan Kasashen Da Suke Bugawa Zuwa 64 A Shekarar 2030

by Abba Ibrahim Wada
4 months ago
in Wasanni
0
KOFIN DUNIYA: Za A Kara Yawan Kasashen Da Suke Bugawa Zuwa 64 A Shekarar 2030
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kwallon Kafar Kudancin Amurka (Conmebol) ta gabatar da bukata a hukumance na kara yawan kasashen da za su halarci Gasar Kofin Duniya ta 2030 zuwa kasashe 64.

Hadakar kasashen Sifaniya da Morocco da Portugal ne za su karbi bakuncin gasar, bayan bude ta a kasashen Argentina da Paraguay da kuma Uruguay. Gasar Kofin Duniya ta 2026 ce ta farko da kasashe 48 za su halarta, to amma Conmebol na son a fadada gasar a 2030 domin murna cika shekara 100 da fara gasar a duniya.

  • Kwararru Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Dangane Da Wayewar Kan Sin Da Afirka 
  • Yadda Hukuncin Kotun Koli Ya Kara Dagula Rikicin Shugabanci A PDP Da LP

A cewar shugaban Conmebol, Alejandro Dominguez a wani taro da hukumar ta gudanar ranar Alhamis yin karin zai bai wa kasashen duniya damar kallon gasar, don haka ba wanda za a bari a baya dangane da bikin da za a yi na cika shekara 100 da fara gasar cin kofin duniya. Ya ce sun yarda cewa bikin cika shekara 100 na gasar zai zama na kasaitacce, saboda ba a taba yin irinsa ba.

Shugaban hukumar kwallon kafar Uruguay, Ignacio Alonso ne ya fara gabatar da bukatar a lokacin taron Fifa da aka gudanar cikin watan Maris kuma a cikin wata sanarwa da hukumar Fifa ta fitar ranar Juma’a, ta ce hakkinta ne ta yi nazarin kowace shawara da mambobinsu suka gabatar.

Shugaban hukumar ta FIFA, Gianni Infantino ya halarci taron Conmebol na ranar Alhamis, inda kuma ya bayyana cewa Gasar 2030 za ta zama ”gagaruma” da ba a taba gani ba.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana

‘Yan Wasan Afirka Da Ake Ganin Za Su Yi Abin Kirki A Kakar Bana

A shekarar 2017, aka dauki matakin fadada kasashen da za su halarci gasar 2026 zuwa 48 bayan duka mambobin Fita sun kada kuri’ar amincewa da matakin, sannan a ranar 15 ga watan Mayu mai zuwa ne za a gudanar da taron FIFA na 75, kuma a nan ne za a tattauna bukatar ta Conmebol. Idan har aka amince da bukatar, gasar ta 2030 za ta kunshi karawa 128, daga karawa 64 da ake yi tsakanin 1998 zuwa 2022.

Masu sukar matakin dai na cewa fadada gasar zai rage darajar tsarin da ake bi wajen tantance cancantar shiga gasar, yayin da kungiyar kare muhalli ta FFF ta ce shawarar buga gasar a nahiyoyi uku barazana ce ga muhalli. Tuni dai a farkon watannan shugaban hukumar kwallon kafar Turai, Aleksander Ceferin ya bayyana matakin a matsayin ”mummunar shawara”.

Ya ce wannan shawara ta yiwu ta fi ba shi mamaki fiye da su, domin shi yana ganin wannan shawara ce maras kyau a ra’ayinsa. Za dai a fara gasar 2030 a Uruguay – kasar da ta fara lashe gasar a 1930, a wani bangare na bikin cika shekara 100 da fara gasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KasasheKofin Duniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ma’aikatar Kasuwancin Sin: Dole Ne Amurka Ta Daina Dora Laifi Kan Sauran Kasashe

Next Post

Tsarin BRICS Ya Zama Muhimmin Dandalin Hadin Kai Na Kasashe Masu Tasowa

Related

Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana
Wasanni

Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana

14 hours ago
‘Yan Wasan Afirka Da Ake Ganin Za Su Yi Abin Kirki A Kakar Bana
Wasanni

‘Yan Wasan Afirka Da Ake Ganin Za Su Yi Abin Kirki A Kakar Bana

15 hours ago
Rasmus Højlund Ya Sauya Sheƙa Zuwa Napoli A Matsayin Aro Daga Manchester United
Wasanni

Rasmus Højlund Ya Sauya Sheƙa Zuwa Napoli A Matsayin Aro Daga Manchester United

1 day ago
Tottenham Ta ÆŠauki Xavi Simons Daga RB Leipzig
Wasanni

Tottenham Ta ÆŠauki Xavi Simons Daga RB Leipzig

2 days ago
AC Milan Ta Amince Da Biyan Yuro Miliyan 36 Domin Daukar Nkunku Daga Chelsea
Wasanni

AC Milan Ta Amince Da Biyan Yuro Miliyan 36 Domin Daukar Nkunku Daga Chelsea

3 days ago
Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds
Wasanni

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

6 days ago
Next Post
Tsarin BRICS Ya Zama Muhimmin Dandalin Hadin Kai Na Kasashe Masu Tasowa

Tsarin BRICS Ya Zama Muhimmin Dandalin Hadin Kai Na Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

August 31, 2025
Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

August 31, 2025
Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

August 31, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Farfado Da Kasa Bisa Karfin Ruhin Turjiya Ga Zalunci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Farfado Da Kasa Bisa Karfin Ruhin Turjiya Ga Zalunci

August 31, 2025
Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

August 31, 2025
Kasar Sin Ta Inganta Wuraren Tunawa Da Tarihi Don Bikin Samun Nasara Kan Zaluncin Japanawa

Kasar Sin Ta Inganta Wuraren Tunawa Da Tarihi Don Bikin Samun Nasara Kan Zaluncin Japanawa

August 31, 2025
Jami’an Senegal Sun Yaba Da Ci Gaban Da Aka Samu Wajen Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

Jami’an Senegal Sun Yaba Da Ci Gaban Da Aka Samu Wajen Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

August 31, 2025
Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

August 31, 2025
Fim Din Kasar Sin Kan Kisan Kiyashin Nanjing Ya Ja Hankulan Masu Kallo A Nijeriya

Fim Din Kasar Sin Kan Kisan Kiyashin Nanjing Ya Ja Hankulan Masu Kallo A Nijeriya

August 31, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgi: Babu Batun Zagon-Æ™asa Ga Harkokin Sufurin Jiragen Ƙasan Abuja-Kaduna – Gwamnati

August 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.