ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Dakta Idris Abdulaziz

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Kotu

Babbar Kotun Shari’ar Musulunci da keJihar Bauchi ta bayar da umarnin kamo Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi.

Malamin a kwanakin baya ya fito daga gidan yari bayan shafe sati guda da ya yi a tsare, kan zargin tada zaune tsaye da ke barazana ga zaman lafiyan jihar.

  • Sanatoci 2 Sun Yi Murabus Daga Jam’iyyar PDP
  • Burina Tinubu Ya Tilasta Wa Maza Kara Aure —Rashida Mai Sa’a

‘Yansanda ne suka fara gabatar da shi a kotun majistire, amma daga bisani ma’aikatar shari’a ta Jihar Bauchi ta amshi ragamar shari’ar.

ADVERTISEMENT

Tun da farko dai kotun ta tura shi gidan yari amma daga baya aka sake shi.

Sai dai kuma bayan fitowarsa ne aka sake mayar da shari’ar da ake masa daga kotun majistiren zuwa kotun shari’ar Musulunci, inda aka shiga kotun a ranar Laraba.

LABARAI MASU NASABA

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

A zaman da kotun da aka yi a ranar Laraba, alkalin kotun, Malam Hussaini Turaki, ya nuna rashin jin dadinsa bisa kasa amsa gayyatar da kotun ta yi wa Malamin domin amsa Shari’ar da ke gabansa.

Lauyoyin Malamin dai sun shaida wa kotun cewa, a daren jiya rashin lafiya ta riski Malamin, don haka ba zai iya samun damar halartar zaman kotun ba.

Da aka nemi su bayar da takardar tabbacin rashin lafiya daga wani alkali hakan bai samu ba.

Lauyan gwamnatin jihar masu shigar da kara ya bukaci kotun da ta bayar da umarnin kamo Malamin a duk inda aka yi tozali da shi.

Da yake yanke hukunci kan bukatar, alkali Malam Hussaini Turaki ya ce rashin amsa gayyatar tamkarar rashin daraja kotun ne.

Barista Aliyu Ibn Idris, Babban Lauyan gwamnatin Jihar Bauchi, ya shaida wa manema labarai cewa, wanda ake kara bai bayyana a kotun ba, amma ya shigar da bukatar cewa kotun ba ta da hurumin sauraren karar da ake masa ta bakin lauyoyinsa.

“Mu kuma muka yi jayayyar cewa dole ne ya fara bayyana a gaban kotun sai ya gabatar da bukatar cewa kotun ba ta da hurumin sauraron karar.

“Amma da yake bai zo kotun ba, mun gabatar da bukatar a cafko shi tun da ya ki zuwa gaban kotu. Kuma kotun ta amince da wannan bukatar ta mu. Don haka yanzu ko ta dage cikin da sauraron karar zuwa ranar Litinin domin cigaba da sauraro.”

Shi kuma Lauyan malamin, Sadik Abubakar Ilelah, ya ce, sun bukaci a bai wa malamin wata rana domin ya samu damar zuwa amma kotun ta ki amince da hakan, ya ce ba wai sun ki mutunta gayyatar kotun ba ne, illa wanda suke karewan baya da lafiya ne.

A cewarsa, “An sauyo shari’ar ne domin ambato daga kotun majistire zuwa kotun shari’ar musulunci, amma wanda muke karewa bai samu zuwa kotu ba domin rashin lafiyar da yake fama da ita, don haka ba zai zai samu halartar zaman kotun na yau ba. Mun roki a ba shi wani ranar da zai samu ya zo tun da yau ne a ranar farko da aka fara sauraron karar, amma sun ki amince da bukatar da cewa mun ki biyayya wa gayyatar kotu.

“Kotu bayan sauraron muhawarar kowani bangare ta bada umarnin a kamo shi domin ya bayyana bisa dole.”

Baristan ya ce za su yi tunanin daukan matakin da ya dace a bisa amfani da tsarin doka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Ziyarci Wata Makaranta Gabanin Ranar Yara Ta Duniya

Xi Jinping Ya Ziyarci Wata Makaranta Gabanin Ranar Yara Ta Duniya

LABARAI MASU NASABA

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

November 17, 2025
Tinubu

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.