• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Dakta Idris Abdulaziz

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kotu Ta Daure Basarake Shekaru 15 Saboda Garkuwa Da Kansa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar Kotun Shari’ar Musulunci da keJihar Bauchi ta bayar da umarnin kamo Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi.

Malamin a kwanakin baya ya fito daga gidan yari bayan shafe sati guda da ya yi a tsare, kan zargin tada zaune tsaye da ke barazana ga zaman lafiyan jihar.

  • Sanatoci 2 Sun Yi Murabus Daga Jam’iyyar PDP
  • Burina Tinubu Ya Tilasta Wa Maza Kara Aure —Rashida Mai Sa’a

‘Yansanda ne suka fara gabatar da shi a kotun majistire, amma daga bisani ma’aikatar shari’a ta Jihar Bauchi ta amshi ragamar shari’ar.

Tun da farko dai kotun ta tura shi gidan yari amma daga baya aka sake shi.

Sai dai kuma bayan fitowarsa ne aka sake mayar da shari’ar da ake masa daga kotun majistiren zuwa kotun shari’ar Musulunci, inda aka shiga kotun a ranar Laraba.

Labarai Masu Nasaba

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

A zaman da kotun da aka yi a ranar Laraba, alkalin kotun, Malam Hussaini Turaki, ya nuna rashin jin dadinsa bisa kasa amsa gayyatar da kotun ta yi wa Malamin domin amsa Shari’ar da ke gabansa.

Lauyoyin Malamin dai sun shaida wa kotun cewa, a daren jiya rashin lafiya ta riski Malamin, don haka ba zai iya samun damar halartar zaman kotun ba.

Da aka nemi su bayar da takardar tabbacin rashin lafiya daga wani alkali hakan bai samu ba.

Lauyan gwamnatin jihar masu shigar da kara ya bukaci kotun da ta bayar da umarnin kamo Malamin a duk inda aka yi tozali da shi.

Da yake yanke hukunci kan bukatar, alkali Malam Hussaini Turaki ya ce rashin amsa gayyatar tamkarar rashin daraja kotun ne.

Barista Aliyu Ibn Idris, Babban Lauyan gwamnatin Jihar Bauchi, ya shaida wa manema labarai cewa, wanda ake kara bai bayyana a kotun ba, amma ya shigar da bukatar cewa kotun ba ta da hurumin sauraren karar da ake masa ta bakin lauyoyinsa.

“Mu kuma muka yi jayayyar cewa dole ne ya fara bayyana a gaban kotun sai ya gabatar da bukatar cewa kotun ba ta da hurumin sauraron karar.

“Amma da yake bai zo kotun ba, mun gabatar da bukatar a cafko shi tun da ya ki zuwa gaban kotu. Kuma kotun ta amince da wannan bukatar ta mu. Don haka yanzu ko ta dage cikin da sauraron karar zuwa ranar Litinin domin cigaba da sauraro.”

Shi kuma Lauyan malamin, Sadik Abubakar Ilelah, ya ce, sun bukaci a bai wa malamin wata rana domin ya samu damar zuwa amma kotun ta ki amince da hakan, ya ce ba wai sun ki mutunta gayyatar kotun ba ne, illa wanda suke karewan baya da lafiya ne.

A cewarsa, “An sauyo shari’ar ne domin ambato daga kotun majistire zuwa kotun shari’ar musulunci, amma wanda muke karewa bai samu zuwa kotu ba domin rashin lafiyar da yake fama da ita, don haka ba zai zai samu halartar zaman kotun na yau ba. Mun roki a ba shi wani ranar da zai samu ya zo tun da yau ne a ranar farko da aka fara sauraron karar, amma sun ki amince da bukatar da cewa mun ki biyayya wa gayyatar kotu.

“Kotu bayan sauraron muhawarar kowani bangare ta bada umarnin a kamo shi domin ya bayyana bisa dole.”

Baristan ya ce za su yi tunanin daukan matakin da ya dace a bisa amfani da tsarin doka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiDakta IdrisDutsen TanshiKotu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Amsa Wasikar Da Wata Yarinya Yar Bangladesh Ta Rubuta Masa

Next Post

Xi Jinping Ya Ziyarci Wata Makaranta Gabanin Ranar Yara Ta Duniya

Related

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

18 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

18 hours ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

21 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

21 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

2 days ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Manyan Labarai

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

2 days ago
Next Post
Xi Jinping Ya Ziyarci Wata Makaranta Gabanin Ranar Yara Ta Duniya

Xi Jinping Ya Ziyarci Wata Makaranta Gabanin Ranar Yara Ta Duniya

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.