ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Dakta Idris Abdulaziz

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Kotu

Babbar Kotun Shari’ar Musulunci da keJihar Bauchi ta bayar da umarnin kamo Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi.

Malamin a kwanakin baya ya fito daga gidan yari bayan shafe sati guda da ya yi a tsare, kan zargin tada zaune tsaye da ke barazana ga zaman lafiyan jihar.

  • Sanatoci 2 Sun Yi Murabus Daga Jam’iyyar PDP
  • Burina Tinubu Ya Tilasta Wa Maza Kara Aure —Rashida Mai Sa’a

‘Yansanda ne suka fara gabatar da shi a kotun majistire, amma daga bisani ma’aikatar shari’a ta Jihar Bauchi ta amshi ragamar shari’ar.

ADVERTISEMENT

Tun da farko dai kotun ta tura shi gidan yari amma daga baya aka sake shi.

Sai dai kuma bayan fitowarsa ne aka sake mayar da shari’ar da ake masa daga kotun majistiren zuwa kotun shari’ar Musulunci, inda aka shiga kotun a ranar Laraba.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

A zaman da kotun da aka yi a ranar Laraba, alkalin kotun, Malam Hussaini Turaki, ya nuna rashin jin dadinsa bisa kasa amsa gayyatar da kotun ta yi wa Malamin domin amsa Shari’ar da ke gabansa.

Lauyoyin Malamin dai sun shaida wa kotun cewa, a daren jiya rashin lafiya ta riski Malamin, don haka ba zai iya samun damar halartar zaman kotun ba.

Da aka nemi su bayar da takardar tabbacin rashin lafiya daga wani alkali hakan bai samu ba.

Lauyan gwamnatin jihar masu shigar da kara ya bukaci kotun da ta bayar da umarnin kamo Malamin a duk inda aka yi tozali da shi.

Da yake yanke hukunci kan bukatar, alkali Malam Hussaini Turaki ya ce rashin amsa gayyatar tamkarar rashin daraja kotun ne.

Barista Aliyu Ibn Idris, Babban Lauyan gwamnatin Jihar Bauchi, ya shaida wa manema labarai cewa, wanda ake kara bai bayyana a kotun ba, amma ya shigar da bukatar cewa kotun ba ta da hurumin sauraren karar da ake masa ta bakin lauyoyinsa.

“Mu kuma muka yi jayayyar cewa dole ne ya fara bayyana a gaban kotun sai ya gabatar da bukatar cewa kotun ba ta da hurumin sauraron karar.

“Amma da yake bai zo kotun ba, mun gabatar da bukatar a cafko shi tun da ya ki zuwa gaban kotu. Kuma kotun ta amince da wannan bukatar ta mu. Don haka yanzu ko ta dage cikin da sauraron karar zuwa ranar Litinin domin cigaba da sauraro.”

Shi kuma Lauyan malamin, Sadik Abubakar Ilelah, ya ce, sun bukaci a bai wa malamin wata rana domin ya samu damar zuwa amma kotun ta ki amince da hakan, ya ce ba wai sun ki mutunta gayyatar kotun ba ne, illa wanda suke karewan baya da lafiya ne.

A cewarsa, “An sauyo shari’ar ne domin ambato daga kotun majistire zuwa kotun shari’ar musulunci, amma wanda muke karewa bai samu zuwa kotu ba domin rashin lafiyar da yake fama da ita, don haka ba zai zai samu halartar zaman kotun na yau ba. Mun roki a ba shi wani ranar da zai samu ya zo tun da yau ne a ranar farko da aka fara sauraron karar, amma sun ki amince da bukatar da cewa mun ki biyayya wa gayyatar kotu.

“Kotu bayan sauraron muhawarar kowani bangare ta bada umarnin a kamo shi domin ya bayyana bisa dole.”

Baristan ya ce za su yi tunanin daukan matakin da ya dace a bisa amfani da tsarin doka.

Kotu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Ziyarci Wata Makaranta Gabanin Ranar Yara Ta Duniya

Xi Jinping Ya Ziyarci Wata Makaranta Gabanin Ranar Yara Ta Duniya

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.