ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Dakta Idris Abdulaziz

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Kotu

Babbar Kotun Shari’ar Musulunci da keJihar Bauchi ta bayar da umarnin kamo Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi.

Malamin a kwanakin baya ya fito daga gidan yari bayan shafe sati guda da ya yi a tsare, kan zargin tada zaune tsaye da ke barazana ga zaman lafiyan jihar.

  • Sanatoci 2 Sun Yi Murabus Daga Jam’iyyar PDP
  • Burina Tinubu Ya Tilasta Wa Maza Kara Aure —Rashida Mai Sa’a

‘Yansanda ne suka fara gabatar da shi a kotun majistire, amma daga bisani ma’aikatar shari’a ta Jihar Bauchi ta amshi ragamar shari’ar.

ADVERTISEMENT

Tun da farko dai kotun ta tura shi gidan yari amma daga baya aka sake shi.

Sai dai kuma bayan fitowarsa ne aka sake mayar da shari’ar da ake masa daga kotun majistiren zuwa kotun shari’ar Musulunci, inda aka shiga kotun a ranar Laraba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

A zaman da kotun da aka yi a ranar Laraba, alkalin kotun, Malam Hussaini Turaki, ya nuna rashin jin dadinsa bisa kasa amsa gayyatar da kotun ta yi wa Malamin domin amsa Shari’ar da ke gabansa.

Lauyoyin Malamin dai sun shaida wa kotun cewa, a daren jiya rashin lafiya ta riski Malamin, don haka ba zai iya samun damar halartar zaman kotun ba.

Da aka nemi su bayar da takardar tabbacin rashin lafiya daga wani alkali hakan bai samu ba.

Lauyan gwamnatin jihar masu shigar da kara ya bukaci kotun da ta bayar da umarnin kamo Malamin a duk inda aka yi tozali da shi.

Da yake yanke hukunci kan bukatar, alkali Malam Hussaini Turaki ya ce rashin amsa gayyatar tamkarar rashin daraja kotun ne.

Barista Aliyu Ibn Idris, Babban Lauyan gwamnatin Jihar Bauchi, ya shaida wa manema labarai cewa, wanda ake kara bai bayyana a kotun ba, amma ya shigar da bukatar cewa kotun ba ta da hurumin sauraren karar da ake masa ta bakin lauyoyinsa.

“Mu kuma muka yi jayayyar cewa dole ne ya fara bayyana a gaban kotun sai ya gabatar da bukatar cewa kotun ba ta da hurumin sauraron karar.

“Amma da yake bai zo kotun ba, mun gabatar da bukatar a cafko shi tun da ya ki zuwa gaban kotu. Kuma kotun ta amince da wannan bukatar ta mu. Don haka yanzu ko ta dage cikin da sauraron karar zuwa ranar Litinin domin cigaba da sauraro.”

Shi kuma Lauyan malamin, Sadik Abubakar Ilelah, ya ce, sun bukaci a bai wa malamin wata rana domin ya samu damar zuwa amma kotun ta ki amince da hakan, ya ce ba wai sun ki mutunta gayyatar kotun ba ne, illa wanda suke karewan baya da lafiya ne.

A cewarsa, “An sauyo shari’ar ne domin ambato daga kotun majistire zuwa kotun shari’ar musulunci, amma wanda muke karewa bai samu zuwa kotu ba domin rashin lafiyar da yake fama da ita, don haka ba zai zai samu halartar zaman kotun na yau ba. Mun roki a ba shi wani ranar da zai samu ya zo tun da yau ne a ranar farko da aka fara sauraron karar, amma sun ki amince da bukatar da cewa mun ki biyayya wa gayyatar kotu.

“Kotu bayan sauraron muhawarar kowani bangare ta bada umarnin a kamo shi domin ya bayyana bisa dole.”

Baristan ya ce za su yi tunanin daukan matakin da ya dace a bisa amfani da tsarin doka.

Kotu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Ziyarci Wata Makaranta Gabanin Ranar Yara Ta Duniya

Xi Jinping Ya Ziyarci Wata Makaranta Gabanin Ranar Yara Ta Duniya

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.