ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Bai Wa Kwamishinan Gona Wa’adin Kwana 2 Ya Dawo Da Tirakta 58 Da Ya Sayar A Zamfara

by Hussein Yero
3 years ago
Kotu

Babbar kotun daukaka kara ta biyu a Jihar Zamfara, wadda mai shari’a Bello Shinkafi ke jagoranta, ta bai wa Kwamishinan Ma’aikatar Gona na jihar umarnin a cikin kwana biyu da ya dawo da tiraktoci 58 da ake zargin ya sayar da su.

Kotun a jiya Ltinin, ta umarci kwamishinan da ya gurfana a gabanta domin yi mata bayanin dalilansa na zuwa ya kwashe tiraktocin duk da maganar na gaban kotu.

  • Mutane 8 Sun Mutu A Ruwa A Jihar Jigawa
  • An Soma Shari’ar Matashin Da Ya Yi Sanadin Yanke Kafar Wata Yarinya A Sakkwato 

Wakilinmu, ya nakalto cewa tiraktocin da ake zargin kwamishinan da sayarwa wata kotu ce ta kama su da nufin yin gwanjonsu don biyan kudin da kamfanin Dunbulun Investment ke bin gwamnatin Jihar Zamfara bashi.

ADVERTISEMENT

Barista Musbahu Salahudini wanda ya ke kare kamfamin Dunbulum, ya yi wa manema labarai karin bayani akan hukuncin kotun, ya ce a shekara ta 2019 kotun daukaka kara ta uku ta yi hukuncin cewa gwamnatin Jihar Zamfara za ta biya kamfanin Dunbulun Investment kudi Naira miliyan dari biyu da ashirin.

Ya ci gaba da cewa a lokacin gwamnatin ta biya miliyan dari da ‘yan kai saura miliyan dari da uku suka rage ba ta biya ba.

LABARAI MASU NASABA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

“Hakan ya sa babbar kotun ta uku ta bada umarni kama kaddarorin gwamnatin a lokacin ta kama wasu motocin gwamnatin da taraktoci Ma’aikatar Gona 58 a cikin watan Disamban na bara da nufin a yi gwanjon motocin don a biya kamfanin Dunbulun kudinsa, kotun ta yi ta jan kafa akan batun sayar da kaddarorin,” In ji barista Musbahu.

Barista Musbahu ya kara da cewa, “Dokar ta bai wa mai kara dama idan alkalin da ke shari’a ba zai yi maka adalci ba to ka kai kara ga kotun gaba wannan ne ya bamu damar kai karar ga kotun daukaka kara ta biyu don neman hakkinmu.

“Kuma mun shigar da kara a kotun gaban ne don tilastawa kotu ta uku ta yi gwanjon kayan da aka kama da nufin biyan mu hakkokinmu.

“Ana haka sai muka samu labarin cewa, kwamishinan gona ya kwashe taraktocin 58 ya saida. Akan haka ne muka shigar da kara don mu shaida wa mai shari’a Bello Shinkafi a gaban lauyan gwamnatin aka yi hakan ba wanda ya musa.”

Lauyan ya ci gaba da cewa bayan shigar da kokensu ne ya sanya mai shari’a Bello Shinkafi ya amsa bukatarsu na kwamishinan gona da ya gaggauta kawo taraktoci 58 gaban kotun cikin kwana biyu kuma ya mika kansa a gaban kotun a ranar 14/9/2022, don ya kare kansa akan wasa da shiri’a da ya yi ta yadda motoci na gaban kotun zai kwashe ya sayar.

‘Yan jaridu sun nemi jin ta bakin lauyan gwamnati Jihar Zamfara, inda ya bayyana masu cewa bai fa hurumin yin magana da su sai da umarni kwamishinan shari’a na Jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,
Kasashen Ketare

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Next Post
Miyetti Allah Ta Roki Soludo Ka Da Ya Soke Kiwon Shanu A Jiharsa

Miyetti Allah Ta Roki Soludo Ka Da Ya Soke Kiwon Shanu A Jiharsa

LABARAI MASU NASABA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.