ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Bai Wa Kwamishinan Gona Wa’adin Kwana 2 Ya Dawo Da Tirakta 58 Da Ya Sayar A Zamfara

by Hussein Yero
3 years ago
Kotu

Babbar kotun daukaka kara ta biyu a Jihar Zamfara, wadda mai shari’a Bello Shinkafi ke jagoranta, ta bai wa Kwamishinan Ma’aikatar Gona na jihar umarnin a cikin kwana biyu da ya dawo da tiraktoci 58 da ake zargin ya sayar da su.

Kotun a jiya Ltinin, ta umarci kwamishinan da ya gurfana a gabanta domin yi mata bayanin dalilansa na zuwa ya kwashe tiraktocin duk da maganar na gaban kotu.

  • Mutane 8 Sun Mutu A Ruwa A Jihar Jigawa
  • An Soma Shari’ar Matashin Da Ya Yi Sanadin Yanke Kafar Wata Yarinya A Sakkwato 

Wakilinmu, ya nakalto cewa tiraktocin da ake zargin kwamishinan da sayarwa wata kotu ce ta kama su da nufin yin gwanjonsu don biyan kudin da kamfanin Dunbulun Investment ke bin gwamnatin Jihar Zamfara bashi.

ADVERTISEMENT

Barista Musbahu Salahudini wanda ya ke kare kamfamin Dunbulum, ya yi wa manema labarai karin bayani akan hukuncin kotun, ya ce a shekara ta 2019 kotun daukaka kara ta uku ta yi hukuncin cewa gwamnatin Jihar Zamfara za ta biya kamfanin Dunbulun Investment kudi Naira miliyan dari biyu da ashirin.

Ya ci gaba da cewa a lokacin gwamnatin ta biya miliyan dari da ‘yan kai saura miliyan dari da uku suka rage ba ta biya ba.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

“Hakan ya sa babbar kotun ta uku ta bada umarni kama kaddarorin gwamnatin a lokacin ta kama wasu motocin gwamnatin da taraktoci Ma’aikatar Gona 58 a cikin watan Disamban na bara da nufin a yi gwanjon motocin don a biya kamfanin Dunbulun kudinsa, kotun ta yi ta jan kafa akan batun sayar da kaddarorin,” In ji barista Musbahu.

Barista Musbahu ya kara da cewa, “Dokar ta bai wa mai kara dama idan alkalin da ke shari’a ba zai yi maka adalci ba to ka kai kara ga kotun gaba wannan ne ya bamu damar kai karar ga kotun daukaka kara ta biyu don neman hakkinmu.

“Kuma mun shigar da kara a kotun gaban ne don tilastawa kotu ta uku ta yi gwanjon kayan da aka kama da nufin biyan mu hakkokinmu.

“Ana haka sai muka samu labarin cewa, kwamishinan gona ya kwashe taraktocin 58 ya saida. Akan haka ne muka shigar da kara don mu shaida wa mai shari’a Bello Shinkafi a gaban lauyan gwamnatin aka yi hakan ba wanda ya musa.”

Lauyan ya ci gaba da cewa bayan shigar da kokensu ne ya sanya mai shari’a Bello Shinkafi ya amsa bukatarsu na kwamishinan gona da ya gaggauta kawo taraktoci 58 gaban kotun cikin kwana biyu kuma ya mika kansa a gaban kotun a ranar 14/9/2022, don ya kare kansa akan wasa da shiri’a da ya yi ta yadda motoci na gaban kotun zai kwashe ya sayar.

‘Yan jaridu sun nemi jin ta bakin lauyan gwamnati Jihar Zamfara, inda ya bayyana masu cewa bai fa hurumin yin magana da su sai da umarni kwamishinan shari’a na Jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir
Labarai

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Next Post
Miyetti Allah Ta Roki Soludo Ka Da Ya Soke Kiwon Shanu A Jiharsa

Miyetti Allah Ta Roki Soludo Ka Da Ya Soke Kiwon Shanu A Jiharsa

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.