ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Bai Wa Kwamishinan Gona Wa’adin Kwana 2 Ya Dawo Da Tirakta 58 Da Ya Sayar A Zamfara

by Hussein Yero
4 years ago
Kotu

Babbar kotun daukaka kara ta biyu a Jihar Zamfara, wadda mai shari’a Bello Shinkafi ke jagoranta, ta bai wa Kwamishinan Ma’aikatar Gona na jihar umarnin a cikin kwana biyu da ya dawo da tiraktoci 58 da ake zargin ya sayar da su.

Kotun a jiya Ltinin, ta umarci kwamishinan da ya gurfana a gabanta domin yi mata bayanin dalilansa na zuwa ya kwashe tiraktocin duk da maganar na gaban kotu.

  • Mutane 8 Sun Mutu A Ruwa A Jihar Jigawa
  • An Soma Shari’ar Matashin Da Ya Yi Sanadin Yanke Kafar Wata Yarinya A Sakkwato 

Wakilinmu, ya nakalto cewa tiraktocin da ake zargin kwamishinan da sayarwa wata kotu ce ta kama su da nufin yin gwanjonsu don biyan kudin da kamfanin Dunbulun Investment ke bin gwamnatin Jihar Zamfara bashi.

ADVERTISEMENT

Barista Musbahu Salahudini wanda ya ke kare kamfamin Dunbulum, ya yi wa manema labarai karin bayani akan hukuncin kotun, ya ce a shekara ta 2019 kotun daukaka kara ta uku ta yi hukuncin cewa gwamnatin Jihar Zamfara za ta biya kamfanin Dunbulun Investment kudi Naira miliyan dari biyu da ashirin.

Ya ci gaba da cewa a lokacin gwamnatin ta biya miliyan dari da ‘yan kai saura miliyan dari da uku suka rage ba ta biya ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Hakan ya sa babbar kotun ta uku ta bada umarni kama kaddarorin gwamnatin a lokacin ta kama wasu motocin gwamnatin da taraktoci Ma’aikatar Gona 58 a cikin watan Disamban na bara da nufin a yi gwanjon motocin don a biya kamfanin Dunbulun kudinsa, kotun ta yi ta jan kafa akan batun sayar da kaddarorin,” In ji barista Musbahu.

Barista Musbahu ya kara da cewa, “Dokar ta bai wa mai kara dama idan alkalin da ke shari’a ba zai yi maka adalci ba to ka kai kara ga kotun gaba wannan ne ya bamu damar kai karar ga kotun daukaka kara ta biyu don neman hakkinmu.

“Kuma mun shigar da kara a kotun gaban ne don tilastawa kotu ta uku ta yi gwanjon kayan da aka kama da nufin biyan mu hakkokinmu.

“Ana haka sai muka samu labarin cewa, kwamishinan gona ya kwashe taraktocin 58 ya saida. Akan haka ne muka shigar da kara don mu shaida wa mai shari’a Bello Shinkafi a gaban lauyan gwamnatin aka yi hakan ba wanda ya musa.”

Lauyan ya ci gaba da cewa bayan shigar da kokensu ne ya sanya mai shari’a Bello Shinkafi ya amsa bukatarsu na kwamishinan gona da ya gaggauta kawo taraktoci 58 gaban kotun cikin kwana biyu kuma ya mika kansa a gaban kotun a ranar 14/9/2022, don ya kare kansa akan wasa da shiri’a da ya yi ta yadda motoci na gaban kotun zai kwashe ya sayar.

‘Yan jaridu sun nemi jin ta bakin lauyan gwamnati Jihar Zamfara, inda ya bayyana masu cewa bai fa hurumin yin magana da su sai da umarni kwamishinan shari’a na Jihar.

Kotu
Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Miyetti Allah Ta Roki Soludo Ka Da Ya Soke Kiwon Shanu A Jiharsa

Miyetti Allah Ta Roki Soludo Ka Da Ya Soke Kiwon Shanu A Jiharsa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.