ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Bai Wa Kwamishinan Gona Wa’adin Kwana 2 Ya Dawo Da Tirakta 58 Da Ya Sayar A Zamfara

by Hussein Yero
4 years ago
Kotu

Babbar kotun daukaka kara ta biyu a Jihar Zamfara, wadda mai shari’a Bello Shinkafi ke jagoranta, ta bai wa Kwamishinan Ma’aikatar Gona na jihar umarnin a cikin kwana biyu da ya dawo da tiraktoci 58 da ake zargin ya sayar da su.

Kotun a jiya Ltinin, ta umarci kwamishinan da ya gurfana a gabanta domin yi mata bayanin dalilansa na zuwa ya kwashe tiraktocin duk da maganar na gaban kotu.

  • Mutane 8 Sun Mutu A Ruwa A Jihar Jigawa
  • An Soma Shari’ar Matashin Da Ya Yi Sanadin Yanke Kafar Wata Yarinya A Sakkwato 

Wakilinmu, ya nakalto cewa tiraktocin da ake zargin kwamishinan da sayarwa wata kotu ce ta kama su da nufin yin gwanjonsu don biyan kudin da kamfanin Dunbulun Investment ke bin gwamnatin Jihar Zamfara bashi.

ADVERTISEMENT

Barista Musbahu Salahudini wanda ya ke kare kamfamin Dunbulum, ya yi wa manema labarai karin bayani akan hukuncin kotun, ya ce a shekara ta 2019 kotun daukaka kara ta uku ta yi hukuncin cewa gwamnatin Jihar Zamfara za ta biya kamfanin Dunbulun Investment kudi Naira miliyan dari biyu da ashirin.

Ya ci gaba da cewa a lokacin gwamnatin ta biya miliyan dari da ‘yan kai saura miliyan dari da uku suka rage ba ta biya ba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

“Hakan ya sa babbar kotun ta uku ta bada umarni kama kaddarorin gwamnatin a lokacin ta kama wasu motocin gwamnatin da taraktoci Ma’aikatar Gona 58 a cikin watan Disamban na bara da nufin a yi gwanjon motocin don a biya kamfanin Dunbulun kudinsa, kotun ta yi ta jan kafa akan batun sayar da kaddarorin,” In ji barista Musbahu.

Barista Musbahu ya kara da cewa, “Dokar ta bai wa mai kara dama idan alkalin da ke shari’a ba zai yi maka adalci ba to ka kai kara ga kotun gaba wannan ne ya bamu damar kai karar ga kotun daukaka kara ta biyu don neman hakkinmu.

“Kuma mun shigar da kara a kotun gaban ne don tilastawa kotu ta uku ta yi gwanjon kayan da aka kama da nufin biyan mu hakkokinmu.

“Ana haka sai muka samu labarin cewa, kwamishinan gona ya kwashe taraktocin 58 ya saida. Akan haka ne muka shigar da kara don mu shaida wa mai shari’a Bello Shinkafi a gaban lauyan gwamnatin aka yi hakan ba wanda ya musa.”

Lauyan ya ci gaba da cewa bayan shigar da kokensu ne ya sanya mai shari’a Bello Shinkafi ya amsa bukatarsu na kwamishinan gona da ya gaggauta kawo taraktoci 58 gaban kotun cikin kwana biyu kuma ya mika kansa a gaban kotun a ranar 14/9/2022, don ya kare kansa akan wasa da shiri’a da ya yi ta yadda motoci na gaban kotun zai kwashe ya sayar.

‘Yan jaridu sun nemi jin ta bakin lauyan gwamnati Jihar Zamfara, inda ya bayyana masu cewa bai fa hurumin yin magana da su sai da umarni kwamishinan shari’a na Jihar.

Kotu
Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Matawalle Ya Buƙaci Magoya Bayansa Su Mara Wa Shugaba Tinubu, Gwamna Lawal Baya
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Majalisar Zamfara Ta Dakatar Da Shugabannin Kananan Hukumomi Biyu Kan Zargin Almundahanar Kuɗaɗe

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Miyetti Allah Ta Roki Soludo Ka Da Ya Soke Kiwon Shanu A Jiharsa

Miyetti Allah Ta Roki Soludo Ka Da Ya Soke Kiwon Shanu A Jiharsa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.