• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Fara Sauraren Shari’ar Raba Auren ‘Yar Ganduje A Kano

by Abubakar Abba
3 years ago
Kotu

Alkalin babbar kotun shari’a Musulunci da ke Jihar Kano, mai shari’a Abdullahi Halliru, ya yi watsi da bukatar da lauyan da ke kare Inuwa Uba mijin.

Asiya, ‘yar cikin gwamnan Kano, Abudullahi Umar Ganduje, na kalubantar da lauyan cewa kotun ba ta da hurumin sauraren karar.

  • Rikicin Warware Rawanin Tsohon Wazirin Bauchi Na Ci Gaba Da Daukar Sabon Salo
  • Asalin Abin Da Ya Faru Tsakanin Abba Gida-gida Da Uwargidan Shugaban DSS

Asiya ta shigar da karar ne, ta hanyar lauyanta Barista Ibrahim Nassarawa, inda ta bukaci kotun da ta raba aurenta da Inuwa ta hanyar Khul’i.

Asiya dai, a cikin bukatar da ta bai wa kotun, ta ce, a shirye take ta biya Inuwa sadakin auren da ya ba ta Naira 50,000.

A yayin da kotun ta dawo sake sauraren karar a zaman da ta yi a ranar Alhamis domin yanke hukunci a kan takadar karar ta Asiya, alkalin kotun, ya bayyana cewa, kotunsa na da hurumin sauraren karar.

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

Alkalin ya kuma tambayi lauyan wanda ake karar cewar, ko ya san nawa ne Inuwa ya biya a matsayin sadakin Asiya lokacin da aka daura auren, inda lauyan ya shaida wa alkalin cewar ba shi da masaniya.

Lauyan wanda ake karar da kuma wanda ke tsayawa, sun bukaci kotun ta dan tsahirta musu don su Asiya da mijin nata Inuwa don sanin nawa ne adadin sadakin, inda kotun ta amsa bukatar tasu.

Kowanensu ya fita daga cikin dakin kotun don buga wayar tafi da gidanka ga wadanda suke karewa a gaban kotu.

Bayan da kotun ta dawo daga gajeren hutu, lauyan wanda ake karar ya shaida wa kotun cewa, bai samu wanda yake karewa a waya ba, inda ya bukaci kotun ta dage sauraren karar don ya samu ya ji daga bakin wanda ya ke karewa kan nawa ya biya sadakin.

A nasa bangaren lauyan da ke tsayawa mai karar ya hakikance cewa, Inuwa ya bai wa Asiya Naira 50,000 a matsayin sadakin aurenta, inda ya ce, Asiya ta ce, a shirye take ta biya Inuwa Naira 50,000 don a raba auren nasu.

Bayan kammala sauraren duk bangarorin biyu, alkalin kotun ya dage sauraren karar zuwa ranar 19 ga watan Janairu 2023, domin lauyan wanda ake karar ya samu shaidawa kotun adadin sadakin auren da Inuwa ya bai wa Asiya kafin alkalin ya shiga mataki na gaba a kan shari’ar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC
Manyan Labarai

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Next Post
Ya Kashe Matarsa Saboda Rikici Kan Burodi A Legas

Ya Kashe Matarsa Saboda Rikici Kan Burodi A Legas

LABARAI MASU NASABA

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

October 16, 2025
Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.