• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Fara Sauraren Shari’ar Raba Auren ‘Yar Ganduje A Kano

by Abubakar Abba
3 years ago
Kotu

Alkalin babbar kotun shari’a Musulunci da ke Jihar Kano, mai shari’a Abdullahi Halliru, ya yi watsi da bukatar da lauyan da ke kare Inuwa Uba mijin.

Asiya, ‘yar cikin gwamnan Kano, Abudullahi Umar Ganduje, na kalubantar da lauyan cewa kotun ba ta da hurumin sauraren karar.

  • Rikicin Warware Rawanin Tsohon Wazirin Bauchi Na Ci Gaba Da Daukar Sabon Salo
  • Asalin Abin Da Ya Faru Tsakanin Abba Gida-gida Da Uwargidan Shugaban DSS

Asiya ta shigar da karar ne, ta hanyar lauyanta Barista Ibrahim Nassarawa, inda ta bukaci kotun da ta raba aurenta da Inuwa ta hanyar Khul’i.

Asiya dai, a cikin bukatar da ta bai wa kotun, ta ce, a shirye take ta biya Inuwa sadakin auren da ya ba ta Naira 50,000.

A yayin da kotun ta dawo sake sauraren karar a zaman da ta yi a ranar Alhamis domin yanke hukunci a kan takadar karar ta Asiya, alkalin kotun, ya bayyana cewa, kotunsa na da hurumin sauraren karar.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Alkalin ya kuma tambayi lauyan wanda ake karar cewar, ko ya san nawa ne Inuwa ya biya a matsayin sadakin Asiya lokacin da aka daura auren, inda lauyan ya shaida wa alkalin cewar ba shi da masaniya.

Lauyan wanda ake karar da kuma wanda ke tsayawa, sun bukaci kotun ta dan tsahirta musu don su Asiya da mijin nata Inuwa don sanin nawa ne adadin sadakin, inda kotun ta amsa bukatar tasu.

Kowanensu ya fita daga cikin dakin kotun don buga wayar tafi da gidanka ga wadanda suke karewa a gaban kotu.

Bayan da kotun ta dawo daga gajeren hutu, lauyan wanda ake karar ya shaida wa kotun cewa, bai samu wanda yake karewa a waya ba, inda ya bukaci kotun ta dage sauraren karar don ya samu ya ji daga bakin wanda ya ke karewa kan nawa ya biya sadakin.

A nasa bangaren lauyan da ke tsayawa mai karar ya hakikance cewa, Inuwa ya bai wa Asiya Naira 50,000 a matsayin sadakin aurenta, inda ya ce, Asiya ta ce, a shirye take ta biya Inuwa Naira 50,000 don a raba auren nasu.

Bayan kammala sauraren duk bangarorin biyu, alkalin kotun ya dage sauraren karar zuwa ranar 19 ga watan Janairu 2023, domin lauyan wanda ake karar ya samu shaidawa kotun adadin sadakin auren da Inuwa ya bai wa Asiya kafin alkalin ya shiga mataki na gaba a kan shari’ar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Triumph
Manyan Labarai

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Next Post
Ya Kashe Matarsa Saboda Rikici Kan Burodi A Legas

Ya Kashe Matarsa Saboda Rikici Kan Burodi A Legas

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.