ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Faru Tsakanin Abba Gida-gida Da Uwargidan Shugaban DSS

by Bello Hamza and Abdullahi Muh'd Sheka
4 years ago
Abba Gida-gida

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

A makon jiya ne aka samu wata takaddama a tsakanin dan takarar gwamnan Jihar Kano a karkashin jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf wanda aka fi sani da Abba Gida-gida da Uwargidar shugaban Hukumar DSS Aisha Yusuf Bichi a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano a yayin da magoya bayan mutanen biyu suka tayar da jijiyar wuya a tsakanin su har ta kai ga furuce-furuce a kafafen sadarwa na zamani, Wakilanmu sun bi diddigi don gano asalin abin da ya faru da kuma yadda abin ya nemi ya tunbatsa har ya kusan daukar sabon salo.

Matar babban daraktan tsaro na farin Kaya na kasa (DSS) ta sa an tsare dan takarar kujerar Gwamnan Kano na Jam’iyyar NNPP na Kano Injiniya Abba Kabir Yusif Wanda a kafi sani da (Abba Gida-gida) tare da bada umarnin lakadawa hadiminsa duka a filin sauka da tashin jirgen sama a Malam Aminu Kano.

  • Turkashi: Aisha Bichi Ta Ce Jami’an Tsaron Farin Kaya Su Kamo Mata Abba Gida-Gida

Kamar yadda rahotanni suka nuna mai dakin babban Darakta hukumar jami’an tsaro na farin kaya (DSS), Aisha Yusuf Bichi, ta bada umarnin a tsare dan takarar Gwamnan na jam’iyyar NNPP a Kano, Abba Kabir Yusuf, inda ta hana shi hawa jirgi da ga Kano zuwa Abuja.
Dambarwar ta faru ne a kofar shiga bangaren matafiya masu ido da Kwalli (alfarma) na filin sauka da tashin jirgen sama na Malam Aminu Kano, yayin da ayarin motocin Abba Kabir Yusuf, wanda a ka fi sani da Abba Gida-gida, su ka haifar da cinkoso a lokacin da ita uwargidan Gidan babban Daraktan Hukumar tsaron farin kayan ke Kan hanyarta ta shiga filin Jirgin.
Lamarin da ya haifar wa da ayarin motocin da ke tare a taron Aisha Bichi tsaiko, yayin da ta ke shiga bangaren masu ido da kwallin domin tashi zuwa Abuja.
Wannan cunkoso da motocin wancan dan takara ya haifar ne ya fusata Aisha Bichi, inda dogarawanta su ka rika duka kan mai uwa da wabi da ababen hawa saboda raina Hajiya da suke zargin tawagar wancan dan takara ya yi.
Shaidun gani da ido sun ce da kurar ta lafa, sai shi Injiniya Abba Abba Kabir Yusif (Abba Gida-gida) ya je don ya yi mata korafin abinda dogaranta su ka yi, a matsayin ta na kawar mai dakinsa, inda ta nuna matukar bacin ranta, har ta ke cewa ba za ta bari ya zama Gwamna a Kano ba.
Daga nan dai, in ji majiyoyi, sai ga karin jami’an tsaron farin kaya sun zo, inda su ka tsare Abba Gida-gida har sai da Aisha Bichi ta shiga jirgi ta tashi zuwa Abuja.
Wasu majiyoyin ma sun ce kafin ta tashi zuwa Abuja, a lokacin da ta ke ta fada, Aisha Bichi ta hango wani hadimin Abba Gida-gida, Garba Kilo yana daukar ta a waya, inda ta sa dogaran ta su “Harbe shi kuma ba abin da za a yi.” a cewar majiyar data nemi a sakaya sunanta.
Uwar Gidan babban Daraktan Hukumar tsaron farin kayan ta ci gaba da fada, ta kuma rantse cewa Abba Gida-gida ba zai shiga jirgi daya da ita ba. Haka dai aka ci gaba da tsare Abba har sai da jirgin ya tashi da matar Daraktan,” in ji majiyar.
Lamarin ya faru ranar Lahadin data gabata, amma kuma wata majiya da bamu tabbatar da sahihancinta ta rawaito cewa, Uwargidan Daraktan Hukumar tsaron farin kayan ta je har gida inda ta baiwa shi Abba Kabir Yusif hakuri bayan jan kunenta da maigidanta ya yi tare da umartarta take ta bashi hakuri.
Alhaji Abba Gwale shima ya yi tsokaci Kan wannan sabata juyetan da ke kara haska wani lamari da ke bukatar yi wa kallon tsanaki, inda ya bayyana cewa, Duk Nijeriya mutane 15 doka ta sahalewa yin amfani da jiniya (Amsa Kuwwa). A ciki babu shugaban jami’an tsaro na farin kaya ballantana matar sa, kuma hukuncin yin amfani da jiniya ga wanda doka bata amince masa ba.
A wani bangare kuma, Shugaban hukumar DSS Yusuf Magaji Bichi, ya bayyana cewa, ya bayyana cewa, ya gano wani shiri na musamman da wasu suka nyi don bata masa suna dana iyalansa, wannan kuma yana faruwa ne saboda mastayarsa ba kan wasu kururin gwamnati da kuma yadda yake gabatar da aikinsa ba tare da tsoro ba.
Ya ce wadannan mutane sun shirya amfani da kungiyoyi masu zaman kansu wajen shirya zanga-zanga da taruka inda za su yi kokarin bata masa suna dana iyalansa.
Yusuf Bichi ya na magana ne a takardar sanarwa da mai magana da yawujn hukumar DSS, Peter Afunanya ya sanya wa hannun aka kuma raba wa manema labarai a Abuja. Ya kuma tabbatar da faruwar takaddama a tsakanin matar Yusuf Bichi da dan takarar gwamnan Jihar kano na jami’iyyar NNPP a filin jigin saman a Malam Aminu Kano inda jami’an DSS da ke rakiyar Aisha Bich suka dakatar da Abba Gida-gida shiga jirgin saman, suna mayar da martani ne bayan da motocin da ke cikin tawagar Abba Gida-gida suka tare hanya abin da ya jawo wa Aisha Bichi jinkiri ita da jama’ar ta.
Sanarwa ta kara da cewa, “Hukumar DSS ba za ta zura ido tana kallon wasu gungun jama’a suna furucin raini ga shugaban da ma’aiakatan hukumar ba saboda wata mastalar da suke fuskanta, kuna kuma kira ga al’umma da su yi watsi da duk wata farfaganda na batanci da za a yi na bata sunan shugaban hukumar.
“Muna kuma kara jaddada goyon bayanmu ga shugaban kasa za kuma mu ci gaba da fuskantar duk wata barazana da ke nemi kawo cikas ga zaman lafiyar kasar nan musamman zaben da ke tafe a cikin wannan shekarar.” In ji sanarwar.

ADVERTISEMENT
Abba Gida-gida
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
Abba Gida-gida
Abdullahi Muh'd Sheka
+ posts Bio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Boko Haram Damfara Ce Da Aka Shirya Don Tarwatsa Nijeriya Kawai -Buhari

Boko Haram Damfara Ce Da Aka Shirya Don Tarwatsa Nijeriya Kawai -Buhari

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.