• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Hana EFCC Kama Rabi’u Musa Kwankwaso

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Kotu Ta Hana EFCC Kama Rabi’u Musa Kwankwaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar kotu a Kano ta bayar da umarnin hana hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa (EFCC) kama Sanata Rabi’u Kwankwaso da wasu mutane shida.

Alkalin kotun mai shari’a Yusuf Ubale Muhammad ne ya bayar da wannan umarni, inda ya haramtawa hukumar EFCC kamawa, da tursasa, da tsarewa, da kuma tsoratarwa, har sai an saurari ƙarar da kuma tantance buƙatar da aka shigar a ranar 5 ga watan Yuni 2024. Wannan hukuncin ya zo ne a yayin da ake ci gaba da bincike.

  • Ko Tinubu Zai Hakura Da Ganduje Ya Rungumi Kwankwaso?
  • Wata Sabuwa: EFCC Ta Buɗe Littafin Kwankwaso

EFCC na zargin karkatar da kuɗaɗen yaƙin neman zaɓe da suka kai Naira biliyan ₦2.5b da tsohon ɗan takarar shugabancin ƙasa na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) ya yi.

Umurnin wucin gadi na Mai shari’a Muhammad ya tabbatar da cewa hukumar EFCC, da jami’anta, da duk wani bangare da ke da alaka da su an hana su cin zarafin masu ƙara.

Alkalin kotun ya bayar da umarnin a mika wa EFCC umarnin na wucin gadi tare da bukatar da aka gabatar a kan sanarwa da duk wasu takardun da suka dace a mika su ga hukumar ta EFCC nan take kafin ranar da za a dawo kotu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

A ranar 24 ga watan Yunin 2024 ne za a ci gaba da sauraren shari’ar a kan ƙudirin da aka gabatar, wanda zai ƙara tantance shari’ar da hukumar EFCC ta yi wa Kwankwaso da sauran mutanen da abin ya shafa.

Sakamakon zaman da za a yi a ranar 24 ga watan Yuni zai kasance muhimmi wajen tantance ko EFCC za ta iya ci gaba da gudanar da ayyukanta ko kuma dokar hana kama shi ta ci gaba da aiki, ta yadda za a kare Kwankwaso da mukarrabansa daga yiwuwar kamawa da gurfanarwa a gaban kuliya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EFCCkanoKwankwaso
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jirgin Ƙarshe Na Maniyyatan Nigeriya Ya Isa Madina

Next Post

UNAOC Ya Yi Maraba Da Kudurin Da Sin Ta Gabatar Na Ayyana Ranar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Al’ummomi Ta Duniya

Related

‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

4 weeks ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

4 weeks ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

3 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

4 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

4 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

4 months ago
Next Post
UNAOC Ya Yi Maraba Da Kudurin Da Sin Ta Gabatar Na Ayyana Ranar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Al’ummomi Ta Duniya

UNAOC Ya Yi Maraba Da Kudurin Da Sin Ta Gabatar Na Ayyana Ranar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Al’ummomi Ta Duniya

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

June 26, 2025
Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

June 26, 2025
Kawayen amarya

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.