• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Hana EFCC Kama Rabi’u Musa Kwankwaso

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Kwankwaso

Wata babbar kotu a Kano ta bayar da umarnin hana hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa (EFCC) kama Sanata Rabi’u Kwankwaso da wasu mutane shida.

Alkalin kotun mai shari’a Yusuf Ubale Muhammad ne ya bayar da wannan umarni, inda ya haramtawa hukumar EFCC kamawa, da tursasa, da tsarewa, da kuma tsoratarwa, har sai an saurari ƙarar da kuma tantance buƙatar da aka shigar a ranar 5 ga watan Yuni 2024. Wannan hukuncin ya zo ne a yayin da ake ci gaba da bincike.

  • Ko Tinubu Zai Hakura Da Ganduje Ya Rungumi Kwankwaso?
  • Wata Sabuwa: EFCC Ta Buɗe Littafin Kwankwaso

EFCC na zargin karkatar da kuɗaɗen yaƙin neman zaɓe da suka kai Naira biliyan ₦2.5b da tsohon ɗan takarar shugabancin ƙasa na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) ya yi.

Umurnin wucin gadi na Mai shari’a Muhammad ya tabbatar da cewa hukumar EFCC, da jami’anta, da duk wani bangare da ke da alaka da su an hana su cin zarafin masu ƙara.

Alkalin kotun ya bayar da umarnin a mika wa EFCC umarnin na wucin gadi tare da bukatar da aka gabatar a kan sanarwa da duk wasu takardun da suka dace a mika su ga hukumar ta EFCC nan take kafin ranar da za a dawo kotu.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

A ranar 24 ga watan Yunin 2024 ne za a ci gaba da sauraren shari’ar a kan ƙudirin da aka gabatar, wanda zai ƙara tantance shari’ar da hukumar EFCC ta yi wa Kwankwaso da sauran mutanen da abin ya shafa.

Sakamakon zaman da za a yi a ranar 24 ga watan Yuni zai kasance muhimmi wajen tantance ko EFCC za ta iya ci gaba da gudanar da ayyukanta ko kuma dokar hana kama shi ta ci gaba da aiki, ta yadda za a kare Kwankwaso da mukarrabansa daga yiwuwar kamawa da gurfanarwa a gaban kuliya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
UNAOC Ya Yi Maraba Da Kudurin Da Sin Ta Gabatar Na Ayyana Ranar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Al’ummomi Ta Duniya

UNAOC Ya Yi Maraba Da Kudurin Da Sin Ta Gabatar Na Ayyana Ranar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Al’ummomi Ta Duniya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.