ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Sake Ɗage Shari’ar Sanata Natasha

by Abubakar Sulaiman
4 weeks ago
Kotu

Kotun Tarayya da ke Abuja ta ɗage ci gaban shari’ar Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan zuwa ranar 4 ga Fabrairu 2026, bayan zaman da aka shirya yau Litinin ya ci tura saboda rashin halartar mai shari’a Mohammed Umar. Wannan dai shi ne karo na biyu da ƙarar ke kasa ci gaba, kasancewar a ranar 21 ga Oktoba ma shari’ar ta tsaya ne sakamakon zanga-zangar da Omoyele Sowore ya jagoranta kan neman sakin Nnamdi Kanu. Tun a ranar 22 ga Satumba ne alƙalin ya tsara ci gaban zaman, amma suka tsaya bayan lauyanta ya ƙalubalanci ci gaba da shari’ar.

Sanata Natasha na fuskantar gurfanarwa ne tun a ranar 30 ga Yuni kan tuhume-tuhume shida da ofishin babban mai shigar da ƙara ya gabatar.

  • Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
  • Natasha Ta Jinjinawa ‘Yan Mazaɓarta, NLC, NBA Bayan Ta Koma Ofishinta Na Majalisa 

An bada belinta, sannan aka ware Satumba 22 don fara sauraron shaidu. Sai dai a ranar da aka koma kotu, lauyan gwamnati ya shirya fara gabatar da shaida bayan sanya allon talabijin a ɗakin shari’a, amma lauyanta, Ehiogie West-Idahosa, ya dage cewa kotu ba za ta iya ci gaba da sauraron shari’ar ba saboda sun riga sun shigar da ƙarar ƙalubalantar hurumin kotu. Ya ce matsalar ba a kan tuhume-tuhumen bane kai tsaye, amma a kan abin da ya kira amfani da ikon Babban Lauyan Kasa ba bisa ƙa’ida ba.

ADVERTISEMENT

Lauyan ya kuma koka cewa ba a miƙawa bangarensu kwafin bayanan shaidun gwamnati ba, abin da ya saɓawa yadda ake yanke shawara cikin adalci. Duk da cewa lauyan gwamnati David Kaswe ya nemi kotu ta ci gaba da shari’a, mai shari’a Umar ya dage cewa dole ne a fara sauraron wannan ƙalubale kafin komawa ga shaida. Alƙalin ya ce dole ne kotu ta fara yanke hukunci kan ikon da ake ƙalubalantarta, kafin a bi mataki na gaba a cikin shari’ar.

A cikin takardar tuhume-tuhumen, ana zargin Sanata Natasha da aikawa da bayanan karya da ke iya cutarwa ta hanyar sadarwa da nufin tayar da hankula da jefa rayuka cikin haɗari.

LABARAI MASU NASABA

Cikin Sauƙi Na Yanke Shawarar Komawa APC – Gwamna Fubara

Ba Zan Taɓa Komawa Jam’iyyar APC Ba — Abaribe

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Siyasa

Cikin Sauƙi Na Yanke Shawarar Komawa APC – Gwamna Fubara

December 18, 2025
Ba Zan Taɓa Komawa Jam’iyyar APC Ba — Abaribe
Siyasa

Ba Zan Taɓa Komawa Jam’iyyar APC Ba — Abaribe

December 16, 2025
El-Rufai Ya Ƙaryata Rahoton Goyon Bayan Yanki Ko Wani Mutum A Zaɓen 2027
Siyasa

El-Rufai Ya Ƙaryata Rahoton Goyon Bayan Yanki Ko Wani Mutum A Zaɓen 2027

December 15, 2025
Next Post
Sin Da Afrika Ta Kudu Sun Fitar Da Shawarar Hadin Gwiwa Ta Goyon Bayan Zamanantar Da Kasashen Afrika

Sin Da Afrika Ta Kudu Sun Fitar Da Shawarar Hadin Gwiwa Ta Goyon Bayan Zamanantar Da Kasashen Afrika

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.