ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Sake Ɗage Shari’ar Sanata Natasha

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
Kotu

Kotun Tarayya da ke Abuja ta ɗage ci gaban shari’ar Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan zuwa ranar 4 ga Fabrairu 2026, bayan zaman da aka shirya yau Litinin ya ci tura saboda rashin halartar mai shari’a Mohammed Umar. Wannan dai shi ne karo na biyu da ƙarar ke kasa ci gaba, kasancewar a ranar 21 ga Oktoba ma shari’ar ta tsaya ne sakamakon zanga-zangar da Omoyele Sowore ya jagoranta kan neman sakin Nnamdi Kanu. Tun a ranar 22 ga Satumba ne alƙalin ya tsara ci gaban zaman, amma suka tsaya bayan lauyanta ya ƙalubalanci ci gaba da shari’ar.

Sanata Natasha na fuskantar gurfanarwa ne tun a ranar 30 ga Yuni kan tuhume-tuhume shida da ofishin babban mai shigar da ƙara ya gabatar.

  • Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
  • Natasha Ta Jinjinawa ‘Yan Mazaɓarta, NLC, NBA Bayan Ta Koma Ofishinta Na Majalisa 

An bada belinta, sannan aka ware Satumba 22 don fara sauraron shaidu. Sai dai a ranar da aka koma kotu, lauyan gwamnati ya shirya fara gabatar da shaida bayan sanya allon talabijin a ɗakin shari’a, amma lauyanta, Ehiogie West-Idahosa, ya dage cewa kotu ba za ta iya ci gaba da sauraron shari’ar ba saboda sun riga sun shigar da ƙarar ƙalubalantar hurumin kotu. Ya ce matsalar ba a kan tuhume-tuhumen bane kai tsaye, amma a kan abin da ya kira amfani da ikon Babban Lauyan Kasa ba bisa ƙa’ida ba.

ADVERTISEMENT

Lauyan ya kuma koka cewa ba a miƙawa bangarensu kwafin bayanan shaidun gwamnati ba, abin da ya saɓawa yadda ake yanke shawara cikin adalci. Duk da cewa lauyan gwamnati David Kaswe ya nemi kotu ta ci gaba da shari’a, mai shari’a Umar ya dage cewa dole ne a fara sauraron wannan ƙalubale kafin komawa ga shaida. Alƙalin ya ce dole ne kotu ta fara yanke hukunci kan ikon da ake ƙalubalantarta, kafin a bi mataki na gaba a cikin shari’ar.

A cikin takardar tuhume-tuhumen, ana zargin Sanata Natasha da aikawa da bayanan karya da ke iya cutarwa ta hanyar sadarwa da nufin tayar da hankula da jefa rayuka cikin haɗari.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

Kotu
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Kotu
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Sin Da Afrika Ta Kudu Sun Fitar Da Shawarar Hadin Gwiwa Ta Goyon Bayan Zamanantar Da Kasashen Afrika

Sin Da Afrika Ta Kudu Sun Fitar Da Shawarar Hadin Gwiwa Ta Goyon Bayan Zamanantar Da Kasashen Afrika

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.