ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Sake Ɗage Shari’ar Sanata Natasha

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
Kotu

Kotun Tarayya da ke Abuja ta ɗage ci gaban shari’ar Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan zuwa ranar 4 ga Fabrairu 2026, bayan zaman da aka shirya yau Litinin ya ci tura saboda rashin halartar mai shari’a Mohammed Umar. Wannan dai shi ne karo na biyu da ƙarar ke kasa ci gaba, kasancewar a ranar 21 ga Oktoba ma shari’ar ta tsaya ne sakamakon zanga-zangar da Omoyele Sowore ya jagoranta kan neman sakin Nnamdi Kanu. Tun a ranar 22 ga Satumba ne alƙalin ya tsara ci gaban zaman, amma suka tsaya bayan lauyanta ya ƙalubalanci ci gaba da shari’ar.

Sanata Natasha na fuskantar gurfanarwa ne tun a ranar 30 ga Yuni kan tuhume-tuhume shida da ofishin babban mai shigar da ƙara ya gabatar.

  • Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
  • Natasha Ta Jinjinawa ‘Yan Mazaɓarta, NLC, NBA Bayan Ta Koma Ofishinta Na Majalisa 

An bada belinta, sannan aka ware Satumba 22 don fara sauraron shaidu. Sai dai a ranar da aka koma kotu, lauyan gwamnati ya shirya fara gabatar da shaida bayan sanya allon talabijin a ɗakin shari’a, amma lauyanta, Ehiogie West-Idahosa, ya dage cewa kotu ba za ta iya ci gaba da sauraron shari’ar ba saboda sun riga sun shigar da ƙarar ƙalubalantar hurumin kotu. Ya ce matsalar ba a kan tuhume-tuhumen bane kai tsaye, amma a kan abin da ya kira amfani da ikon Babban Lauyan Kasa ba bisa ƙa’ida ba.

ADVERTISEMENT

Lauyan ya kuma koka cewa ba a miƙawa bangarensu kwafin bayanan shaidun gwamnati ba, abin da ya saɓawa yadda ake yanke shawara cikin adalci. Duk da cewa lauyan gwamnati David Kaswe ya nemi kotu ta ci gaba da shari’a, mai shari’a Umar ya dage cewa dole ne a fara sauraron wannan ƙalubale kafin komawa ga shaida. Alƙalin ya ce dole ne kotu ta fara yanke hukunci kan ikon da ake ƙalubalantarta, kafin a bi mataki na gaba a cikin shari’ar.

A cikin takardar tuhume-tuhumen, ana zargin Sanata Natasha da aikawa da bayanan karya da ke iya cutarwa ta hanyar sadarwa da nufin tayar da hankula da jefa rayuka cikin haɗari.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

Kotu
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
  • Abubakar Sulaiman
    Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

MASU ALAKA

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Atiku
Siyasa

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

July 2, 2026
Next Post
Sin Da Afrika Ta Kudu Sun Fitar Da Shawarar Hadin Gwiwa Ta Goyon Bayan Zamanantar Da Kasashen Afrika

Sin Da Afrika Ta Kudu Sun Fitar Da Shawarar Hadin Gwiwa Ta Goyon Bayan Zamanantar Da Kasashen Afrika

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Montenegro Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 7, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.