Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja ta yi watsi da ƙorafe-ƙorafe guda biyu da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya shigar dangane da dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan daga majalisar.
Kotun, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Hamman Barka, ta umarci Sanata Akpabio da ya biya Sanata Natasha tara Naira 100,000.
- Wang Yi Ya Gabatar Da Jawabi Albarkacin “Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa” Karo Na Farko Na MDD
- Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar
Kotun ta bayyana cewa ta amince da buƙatar Akpabio na janye ƙorafe-ƙorafen biyu da ya shigar ranar 20 da 25 ga watan Maris, 2025.
Sai dai bayan janyewar, kotun ta kori ƙorafe-ƙorafen gaba ɗaya kuma ta bayar tara ga wanda ake ƙara na farko (wato Sanata Natasha).
Hakazalika, kotun ta ce za a goge lambar ƙarar daga kundin shari’a.
Akpabio ya shigar da buƙatu a gaban kotun inda ya nemi ƙarin lokaci don ɗaukaka ƙara a kan hukuncin da Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke a ranar 10 ga watan Maris, 2025.
Wannan shari’a ta haɗa da Sanata Natasha da ke ƙarar Sakataren Majalisar Tarayya da wasu mutane uku kan dakatar da ita.
Haka kuma, Akpabio ya nemi kotu ta ba shi izini ya ɗaukaka ƙara da kuma dakatar da ci gaba da sauraron shari’ar a Babbar Kotun har sai an yanke hukunci a kotun ɗaukaka ƙara.
Sai dai yanzu da aka janye ƙorafe-ƙorafen kuma kotu ta yi watsi da su, hakan na nufin waɗannan bukatu na Akpabio ba za su ci gaba da sauraron su a a kotun ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp