• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Daukaka Kara Za Ta Fara Sauraren Karar Zaben Gwamnan Kano A Ranar Litinin

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kotun Daukaka Kara Za Ta Fara Sauraren Karar Zaben Gwamnan Kano A Ranar Litinin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun daukaka kara ta Kano ta sanya ranar Litinin 6 ga watan Nuwamba, 2023, domin sauraren karar da Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya shigar, yana kalubalantar hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe ta jihar da ta tsige shi a matsayin gwamnan jihar.

Kotun daukaka kara, a wata sanarwa da aka raba wa manema labarai, ta nuna cewa za a fara sauraren karar mai lamba CA/KN/EP/GOV/KAN/34/2023 a ranar Litinin a kotun daukaka kara da ke Abuja.

  • Gwamna Uba Sani Ya Bayar Da Umurnin Gaggauta Biyan Kudin Wutar Lantarki Na Jami’ar KASU
  • Sake Bude Iyaka: Matsalar Da Manoman Arewacin Nijeriya Za Su Fuskanta

Wadanda ke cikin karar sun hada da Gwamna Yusuf na jam’iyyar NNPP da kuma jam’iyyar adawa ta APC, da dan takararta, Nasir Gawuna, da kuma hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

Idan dai za a iya tunawa dai kotun ta yanke hukuncin ne, inda ta bayyana dan takararta APC, Gawuna a matsayin wanda ya cancanta ya lashe zaben gwamnan jihar Kano da aka gudanar a ranar 18 ga Maris, 2023.

Kotun ta soke zaben Gwamna Yusuf ne bayan soke kuri’unsa 165,663, inda ta ce INEC ba ta sanya hannu ko tambari ba akan kuri’unsa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

Mun Tara KuÉ—i Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Idan za a tuna cewa INEC ta bayyana Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 18 ga watan Maris bayan ya samu kuri’u 1,019,602 yayin da abokin hamayyarsa Gawuna ya samu kuri’u 890,705.

Sai dai kotun sauraron kararrakin zabe ta soke kuri’u 165,663 daga kuri’un Yusuf, wanda ya sa kuri’unsa suka koma 853,939, wanda hakan ya sa Gawuna ya ba shi tazarar kuri’u 30,000.

Sakamakon haka ne, kotun ta bayyana dan takarar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna tare da umartar INEC da ta janye takardar shaidar cin zaben Yusuf tare da bai wa Gawuna na jam’iyyar APC.

Sai dai Gwamna Yusuf da jam’iyyarsa, NNPP da kuma INEC sun garzaya kotun daukaka kara domin kalubalantar hukuncin da kotun ta yanke.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbaAPCGawunakanoKotuNNPP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ruto: Aikin Hadin Gwiwa Karkashin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Kawo Babban Canji Ga Kenya

Next Post

Tarihin Rayuwar Marigayi Sarkin Ibira, Ohoniyi Attah Ado Ibrahim

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

4 hours ago
Mun Tara KuÉ—i Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 
Manyan Labarai

Mun Tara KuÉ—i Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

11 hours ago
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

24 hours ago
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

1 day ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

1 day ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

2 days ago
Next Post
Tarihin Rayuwar Marigayi Sarkin Ibira, Ohoniyi Attah Ado Ibrahim

Tarihin Rayuwar Marigayi Sarkin Ibira, Ohoniyi Attah Ado Ibrahim

LABARAI MASU NASABA

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

September 7, 2025
Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

September 7, 2025
Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

September 7, 2025
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

September 7, 2025
Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

Shawara Ga Matashin Da Matarsa Ta Samu Juna Biyu (1)

September 7, 2025
Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

September 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

September 7, 2025
Arewa

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

September 7, 2025
Da ÆŠumi-É—umi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-É“aci A Ribas

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

September 7, 2025
Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.