ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Daukaka Kara Za Ta Fara Sauraren Karar Zaben Gwamnan Kano A Ranar Litinin

by Sadiq
3 years ago
Kotun

Kotun daukaka kara ta Kano ta sanya ranar Litinin 6 ga watan Nuwamba, 2023, domin sauraren karar da Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya shigar, yana kalubalantar hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe ta jihar da ta tsige shi a matsayin gwamnan jihar.

Kotun daukaka kara, a wata sanarwa da aka raba wa manema labarai, ta nuna cewa za a fara sauraren karar mai lamba CA/KN/EP/GOV/KAN/34/2023 a ranar Litinin a kotun daukaka kara da ke Abuja.

  • Gwamna Uba Sani Ya Bayar Da Umurnin Gaggauta Biyan Kudin Wutar Lantarki Na Jami’ar KASU
  • Sake Bude Iyaka: Matsalar Da Manoman Arewacin Nijeriya Za Su Fuskanta

Wadanda ke cikin karar sun hada da Gwamna Yusuf na jam’iyyar NNPP da kuma jam’iyyar adawa ta APC, da dan takararta, Nasir Gawuna, da kuma hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

ADVERTISEMENT

Idan dai za a iya tunawa dai kotun ta yanke hukuncin ne, inda ta bayyana dan takararta APC, Gawuna a matsayin wanda ya cancanta ya lashe zaben gwamnan jihar Kano da aka gudanar a ranar 18 ga Maris, 2023.

Kotun ta soke zaben Gwamna Yusuf ne bayan soke kuri’unsa 165,663, inda ta ce INEC ba ta sanya hannu ko tambari ba akan kuri’unsa.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Idan za a tuna cewa INEC ta bayyana Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 18 ga watan Maris bayan ya samu kuri’u 1,019,602 yayin da abokin hamayyarsa Gawuna ya samu kuri’u 890,705.

Sai dai kotun sauraron kararrakin zabe ta soke kuri’u 165,663 daga kuri’un Yusuf, wanda ya sa kuri’unsa suka koma 853,939, wanda hakan ya sa Gawuna ya ba shi tazarar kuri’u 30,000.

Sakamakon haka ne, kotun ta bayyana dan takarar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna tare da umartar INEC da ta janye takardar shaidar cin zaben Yusuf tare da bai wa Gawuna na jam’iyyar APC.

Sai dai Gwamna Yusuf da jam’iyyarsa, NNPP da kuma INEC sun garzaya kotun daukaka kara domin kalubalantar hukuncin da kotun ta yanke.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Tarihin Rayuwar Marigayi Sarkin Ibira, Ohoniyi Attah Ado Ibrahim

Tarihin Rayuwar Marigayi Sarkin Ibira, Ohoniyi Attah Ado Ibrahim

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.