ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sake Bude Iyaka: Matsalar Da Manoman Arewacin Nijeriya Za Su Fuskanta

by Abubakar Abba
3 years ago
Iyaka

A shekarar 2019 ne, Tsohon Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari, ya bayar da umarnin garkame daukacin iyakokin Nijeriya.

Tsohuwar gwamnatin, ta kuma bayar da umarnin haramta shigo da wasu kaya cikin wannan kasa da kuma fitar da su daga cikin kasar, musamman kayan abinci domin a kara habaka harkokin noma  a Nijeriya tare da samar da wadataccen abinci a fadin kasa baki-daya.

  • Matar Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar Da Bada Tallafin N50,000 Ga Mata Dubu 4 A Gusau
  • Hadarin Da Ya Auku Ya Bankado Karyar Japan Game Da Ruwan Dagwalon Nukiliyar Da Take Zubarwa A Teku

Barin iyakokin kasar kara zube, shi ne ya jawo tabarwarewar tattalin arzikin Nijeriya shekaru da dama da suka gabata.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, kayan da ake sarrafawa a kasar waje ake shigowa da su cikin Nijeriya, su ne suka tilasata wa masana’antu da dama na cikin gida garkamewa.

Wannan ne ya yi sanadiyyar dubban ma’aikatan da suke aiki a wadannan masana’antu rasa ayyukansu.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ko shakka babu, wannan al’amari a bayyane yake; musamman idan aka yi la’akari da yadda Arewacin wannan kasa ta yi fice wajen habaka fannin tattalin arziki da kuma samar da ayyukan yi ta hanyar aikin noma a Nijeriya.

Har ila yau, karkame iyakokin kasar ya samar da damar samun kara bude masana’antun sarrafa shikafa a Arewacin wannan kasa, wanda hakan ya bayar da damar samun dimbin ayyukan yi a yankin.

Haka zalika, rufe iyakokin ya bai wa ‘Yan Nijeriya da dama rungumar wannan fanni na aikin noma, wanda ya yi sanadiyyar karin samar da wadataccen abinci a daukacin fadin kasar.

Misali, daga watan Junairu zuwa na Maris din shekarar 2021, fannin aikin noma ya bayar da gagarumar gudunmawa ga tattalin arzikin Nijeriya, wanda ya kai har kashi 22.35 cikin dari na jumullar tattalin arzikin Nijeriya.

“Rufe iyakokin ya bai wa ‘yan Nijeriya da dama damar rungumar fannin aikin noma, wanda hakan ya sa aka kara samar da wadataccen abinci a daukacin fadin wannan kasa baki-daya.”

Sai dai, wasu ‘Yan Nijeriya da dama, na cike da farin ciki a kan umarnin da Gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayar na sake bude iyakokin Nijeriyan, musamman domin ci gaba da shigo da shinkafa, tumatir da kuma sauran kayayyaki zuwa cikin gida Nijeriya.

Har wa yau, a bangaren manoma musamman wadanda ke Arewacin Nijeriya, wannan umarni na Tinubu zai iya jefa makomar rayuwarsu cikin wani mawuyacin hali.

Kazalika, akasarin mazauna yankin na Arewa wadanda suka dauki sana’ar aikin noma, damina da rani das hi suka dogara.

Sannan, bude iyakokin kasar zai iya kassara kayan da ake sarrafawa a Arewacnin Kasar, wanda akasarin masana’antun ba za su iya yin gasa da kayan da ake  sarrafawa a  kasashen ketare ba, wanda hakan kuma kai tsaye zai karya farashin kayan amfanin gona na manoman da ke wannan yanki.

“Bugu da kari, sake bude iyakokin wannan kasa, zai  kawo wa kayan da ake sarrafa wa a Arewa babban nakasu, musamman ganin cewa, mafi yawancin masana’antun ba za su iya yin gasa da irin kayan da ake sarrafawa a kasashen ketare ba, wanda hakan kuma zai karya farashin kayan amfanin gonan manoman da ke wannan yanki.”

Sai dai, wasu mutane da ke yankin na Arewa ba sa yin la’akari da yadda ake yakar hare-haren ‘yan bindiga ta kowanne bangare, misali’ tun daga fannin ilimin boko, aikin noma da sauran harkokin kasuwanci.

Don haka, yanzu lokaci ya yi da gwamnatin tarayya ta hanyar Babban Bankin Nijeriya (CBN), za ta sake auna fa’ida da kuma rashin fa’idar sake bude iyakon kasar tare da daukar matakin da zai fi zama mai sauki ga ‘yan Nijeriya.

Iyaka
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Amfanin Kankana Ga Lafiyar Jiki Da Ta Iyali 

Amfanin Kankana Ga Lafiyar Jiki Da Ta Iyali 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.