ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sake Bude Iyaka: Matsalar Da Manoman Arewacin Nijeriya Za Su Fuskanta

by Abubakar Abba
3 years ago
Iyaka

A shekarar 2019 ne, Tsohon Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari, ya bayar da umarnin garkame daukacin iyakokin Nijeriya.

Tsohuwar gwamnatin, ta kuma bayar da umarnin haramta shigo da wasu kaya cikin wannan kasa da kuma fitar da su daga cikin kasar, musamman kayan abinci domin a kara habaka harkokin noma  a Nijeriya tare da samar da wadataccen abinci a fadin kasa baki-daya.

  • Matar Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar Da Bada Tallafin N50,000 Ga Mata Dubu 4 A Gusau
  • Hadarin Da Ya Auku Ya Bankado Karyar Japan Game Da Ruwan Dagwalon Nukiliyar Da Take Zubarwa A Teku

Barin iyakokin kasar kara zube, shi ne ya jawo tabarwarewar tattalin arzikin Nijeriya shekaru da dama da suka gabata.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, kayan da ake sarrafawa a kasar waje ake shigowa da su cikin Nijeriya, su ne suka tilasata wa masana’antu da dama na cikin gida garkamewa.

Wannan ne ya yi sanadiyyar dubban ma’aikatan da suke aiki a wadannan masana’antu rasa ayyukansu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Ko shakka babu, wannan al’amari a bayyane yake; musamman idan aka yi la’akari da yadda Arewacin wannan kasa ta yi fice wajen habaka fannin tattalin arziki da kuma samar da ayyukan yi ta hanyar aikin noma a Nijeriya.

Har ila yau, karkame iyakokin kasar ya samar da damar samun kara bude masana’antun sarrafa shikafa a Arewacin wannan kasa, wanda hakan ya bayar da damar samun dimbin ayyukan yi a yankin.

Haka zalika, rufe iyakokin ya bai wa ‘Yan Nijeriya da dama rungumar wannan fanni na aikin noma, wanda ya yi sanadiyyar karin samar da wadataccen abinci a daukacin fadin kasar.

Misali, daga watan Junairu zuwa na Maris din shekarar 2021, fannin aikin noma ya bayar da gagarumar gudunmawa ga tattalin arzikin Nijeriya, wanda ya kai har kashi 22.35 cikin dari na jumullar tattalin arzikin Nijeriya.

“Rufe iyakokin ya bai wa ‘yan Nijeriya da dama damar rungumar fannin aikin noma, wanda hakan ya sa aka kara samar da wadataccen abinci a daukacin fadin wannan kasa baki-daya.”

Sai dai, wasu ‘Yan Nijeriya da dama, na cike da farin ciki a kan umarnin da Gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayar na sake bude iyakokin Nijeriyan, musamman domin ci gaba da shigo da shinkafa, tumatir da kuma sauran kayayyaki zuwa cikin gida Nijeriya.

Har wa yau, a bangaren manoma musamman wadanda ke Arewacin Nijeriya, wannan umarni na Tinubu zai iya jefa makomar rayuwarsu cikin wani mawuyacin hali.

Kazalika, akasarin mazauna yankin na Arewa wadanda suka dauki sana’ar aikin noma, damina da rani das hi suka dogara.

Sannan, bude iyakokin kasar zai iya kassara kayan da ake sarrafawa a Arewacnin Kasar, wanda akasarin masana’antun ba za su iya yin gasa da kayan da ake  sarrafawa a  kasashen ketare ba, wanda hakan kuma kai tsaye zai karya farashin kayan amfanin gona na manoman da ke wannan yanki.

“Bugu da kari, sake bude iyakokin wannan kasa, zai  kawo wa kayan da ake sarrafa wa a Arewa babban nakasu, musamman ganin cewa, mafi yawancin masana’antun ba za su iya yin gasa da irin kayan da ake sarrafawa a kasashen ketare ba, wanda hakan kuma zai karya farashin kayan amfanin gonan manoman da ke wannan yanki.”

Sai dai, wasu mutane da ke yankin na Arewa ba sa yin la’akari da yadda ake yakar hare-haren ‘yan bindiga ta kowanne bangare, misali’ tun daga fannin ilimin boko, aikin noma da sauran harkokin kasuwanci.

Don haka, yanzu lokaci ya yi da gwamnatin tarayya ta hanyar Babban Bankin Nijeriya (CBN), za ta sake auna fa’ida da kuma rashin fa’idar sake bude iyakon kasar tare da daukar matakin da zai fi zama mai sauki ga ‘yan Nijeriya.

Iyaka
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Amfanin Kankana Ga Lafiyar Jiki Da Ta Iyali 

Amfanin Kankana Ga Lafiyar Jiki Da Ta Iyali 

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.