ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sake Bude Iyaka: Matsalar Da Manoman Arewacin Nijeriya Za Su Fuskanta

by Abubakar Abba
3 years ago
Iyaka

A shekarar 2019 ne, Tsohon Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari, ya bayar da umarnin garkame daukacin iyakokin Nijeriya.

Tsohuwar gwamnatin, ta kuma bayar da umarnin haramta shigo da wasu kaya cikin wannan kasa da kuma fitar da su daga cikin kasar, musamman kayan abinci domin a kara habaka harkokin noma  a Nijeriya tare da samar da wadataccen abinci a fadin kasa baki-daya.

  • Matar Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar Da Bada Tallafin N50,000 Ga Mata Dubu 4 A Gusau
  • Hadarin Da Ya Auku Ya Bankado Karyar Japan Game Da Ruwan Dagwalon Nukiliyar Da Take Zubarwa A Teku

Barin iyakokin kasar kara zube, shi ne ya jawo tabarwarewar tattalin arzikin Nijeriya shekaru da dama da suka gabata.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, kayan da ake sarrafawa a kasar waje ake shigowa da su cikin Nijeriya, su ne suka tilasata wa masana’antu da dama na cikin gida garkamewa.

Wannan ne ya yi sanadiyyar dubban ma’aikatan da suke aiki a wadannan masana’antu rasa ayyukansu.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Ko shakka babu, wannan al’amari a bayyane yake; musamman idan aka yi la’akari da yadda Arewacin wannan kasa ta yi fice wajen habaka fannin tattalin arziki da kuma samar da ayyukan yi ta hanyar aikin noma a Nijeriya.

Har ila yau, karkame iyakokin kasar ya samar da damar samun kara bude masana’antun sarrafa shikafa a Arewacin wannan kasa, wanda hakan ya bayar da damar samun dimbin ayyukan yi a yankin.

Haka zalika, rufe iyakokin ya bai wa ‘Yan Nijeriya da dama rungumar wannan fanni na aikin noma, wanda ya yi sanadiyyar karin samar da wadataccen abinci a daukacin fadin kasar.

Misali, daga watan Junairu zuwa na Maris din shekarar 2021, fannin aikin noma ya bayar da gagarumar gudunmawa ga tattalin arzikin Nijeriya, wanda ya kai har kashi 22.35 cikin dari na jumullar tattalin arzikin Nijeriya.

“Rufe iyakokin ya bai wa ‘yan Nijeriya da dama damar rungumar fannin aikin noma, wanda hakan ya sa aka kara samar da wadataccen abinci a daukacin fadin wannan kasa baki-daya.”

Sai dai, wasu ‘Yan Nijeriya da dama, na cike da farin ciki a kan umarnin da Gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayar na sake bude iyakokin Nijeriyan, musamman domin ci gaba da shigo da shinkafa, tumatir da kuma sauran kayayyaki zuwa cikin gida Nijeriya.

Har wa yau, a bangaren manoma musamman wadanda ke Arewacin Nijeriya, wannan umarni na Tinubu zai iya jefa makomar rayuwarsu cikin wani mawuyacin hali.

Kazalika, akasarin mazauna yankin na Arewa wadanda suka dauki sana’ar aikin noma, damina da rani das hi suka dogara.

Sannan, bude iyakokin kasar zai iya kassara kayan da ake sarrafawa a Arewacnin Kasar, wanda akasarin masana’antun ba za su iya yin gasa da kayan da ake  sarrafawa a  kasashen ketare ba, wanda hakan kuma kai tsaye zai karya farashin kayan amfanin gona na manoman da ke wannan yanki.

“Bugu da kari, sake bude iyakokin wannan kasa, zai  kawo wa kayan da ake sarrafa wa a Arewa babban nakasu, musamman ganin cewa, mafi yawancin masana’antun ba za su iya yin gasa da irin kayan da ake sarrafawa a kasashen ketare ba, wanda hakan kuma zai karya farashin kayan amfanin gonan manoman da ke wannan yanki.”

Sai dai, wasu mutane da ke yankin na Arewa ba sa yin la’akari da yadda ake yakar hare-haren ‘yan bindiga ta kowanne bangare, misali’ tun daga fannin ilimin boko, aikin noma da sauran harkokin kasuwanci.

Don haka, yanzu lokaci ya yi da gwamnatin tarayya ta hanyar Babban Bankin Nijeriya (CBN), za ta sake auna fa’ida da kuma rashin fa’idar sake bude iyakon kasar tare da daukar matakin da zai fi zama mai sauki ga ‘yan Nijeriya.

Iyaka
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Amfanin Kankana Ga Lafiyar Jiki Da Ta Iyali 

Amfanin Kankana Ga Lafiyar Jiki Da Ta Iyali 

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Iyaka

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Iyaka

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.